ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rayukan Mutane Sama Da 86 Suka Salwanta A Kan Titin Nnamdi Azikiwe Da Ke Kaduna

by Alkazeem M. Shariff
1 month ago
Rayukan

Majiya mai tushe ta tabbatar da cewa daga karamar Salla zuwa yau an samu asarar rayuka akalla mutum 86 a babban titin Nnamdi Azikiwe da ke garin Kaduna, wanda aikin gyaran hanyar ya ki ci ya ki cinyewa.

A sakamakon aikin hanyar da ke tafiyar hawainiyya, akasarin wadanda suka rasa rayukansu, manyan motoci ne ke zama ajalinsu, kamar yadda wasu ganau, Dakta Muhammad Jamilu da Injiniya Muhammad Buhari, suka tabbatar mana da hakan.

Malam Muktar mai littafai Dan Mani, yana gudanar da ayyukansa kan babban titin, ya tabbatar da cewa irin abubuwa da ke faruwa a wannan babbar hanyar abin takaici ne, domin akwai ‘yan’uwansa da manyan motocin suka zama ajalinsu har lahira.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, shi ma wani Bawan Allah mai suna Alhaji Nasiru Wagini, wanda shi ma ya bayyana cewa, akwai danuwansa mai suna Dakta Hamza Wagini wanda kemist dinsa ke kasuwar barci Kaduna, shi ma daga zuwa isar da wani muhimmin sako wata babbar mota ta buga kansa da kankaren titin wanda ya yi sanadiyyar rasuwarsa.

A cewarsa, Alhaji Ado Baban Nazifi, mazaunin Unguwar Mu’azu Kaduna, shi ma daga zuwa kai kudin sadaki a Asukulaye kusa da masalacin Sheikh Dahiru Bauci, mota ta kashe shi har lahira.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Ya ce akwai wata mata da goyonta motar tirela ta takesu suka mutu a nan take, haka nan ma a ranar Lahadin da ta gabata, wata motar tirela ta sake halaka wani Bawan Allah mai suna Anas Abdulmumin Kura wanda aka fi sani da Albani, shi da dansa a daidai Kurmin Mashi kusa da sabuwar fanteka. 

Sai dai a kasantuwar rasa rayukan da ake yi a titin ya ta azzara sosai, hakan ya sa wasu mutane sun fara daukar doka a hannunsu, ta yadda wasu matasa ke kona mota da zaran hakan ya faru.

Jama’a da dama sun koka, inda suke kira ga mai girma Gwamna Jihar Kaduna, Malam Uba Sani da ya dube su da idon rahama ya dauki mataki, ya kuma ja hankalin gwamnatin tarayya da ta dauki mataki kawo karshen aikin wannan babbar hanyar, domin dakile cin rayukan al’umma da take yi.

Rayukan
Alkazeem M. Shariff
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnati Ta Amince Da A Dawo Da Tsofaffin Sojoji Fagen Daga

Matsalar Tsaro: Gwamnati Ta Amince Da A Dawo Da Tsofaffin Sojoji Fagen Daga

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.