Majiya mai tushe ta tabbatar da cewa daga karamar Salla zuwa yau an samu asarar rayuka akalla mutum 86 a babban titin Nnamdi Azikiwe da ke garin Kaduna, wanda aikin gyaran hanyar ya ki ci ya ki cinyewa.
A sakamakon aikin hanyar da ke tafiyar hawainiyya, akasarin wadanda suka rasa rayukansu, manyan motoci ne ke zama ajalinsu, kamar yadda wasu ganau, Dakta Muhammad Jamilu da Injiniya Muhammad Buhari, suka tabbatar mana da hakan.
Malam Muktar mai littafai Dan Mani, yana gudanar da ayyukansa kan babban titin, ya tabbatar da cewa irin abubuwa da ke faruwa a wannan babbar hanyar abin takaici ne, domin akwai ‘yan’uwansa da manyan motocin suka zama ajalinsu har lahira.
Haka zalika, shi ma wani Bawan Allah mai suna Alhaji Nasiru Wagini, wanda shi ma ya bayyana cewa, akwai danuwansa mai suna Dakta Hamza Wagini wanda kemist dinsa ke kasuwar barci Kaduna, shi ma daga zuwa isar da wani muhimmin sako wata babbar mota ta buga kansa da kankaren titin wanda ya yi sanadiyyar rasuwarsa.
A cewarsa, Alhaji Ado Baban Nazifi, mazaunin Unguwar Mu’azu Kaduna, shi ma daga zuwa kai kudin sadaki a Asukulaye kusa da masalacin Sheikh Dahiru Bauci, mota ta kashe shi har lahira.
Ya ce akwai wata mata da goyonta motar tirela ta takesu suka mutu a nan take, haka nan ma a ranar Lahadin da ta gabata, wata motar tirela ta sake halaka wani Bawan Allah mai suna Anas Abdulmumin Kura wanda aka fi sani da Albani, shi da dansa a daidai Kurmin Mashi kusa da sabuwar fanteka.
Sai dai a kasantuwar rasa rayukan da ake yi a titin ya ta azzara sosai, hakan ya sa wasu mutane sun fara daukar doka a hannunsu, ta yadda wasu matasa ke kona mota da zaran hakan ya faru.
Jama’a da dama sun koka, inda suke kira ga mai girma Gwamna Jihar Kaduna, Malam Uba Sani da ya dube su da idon rahama ya dauki mataki, ya kuma ja hankalin gwamnatin tarayya da ta dauki mataki kawo karshen aikin wannan babbar hanyar, domin dakile cin rayukan al’umma da take yi.













Discussion about this post