ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rayukan Mutane Sama Da 86 Suka Salwanta A Kan Titin Nnamdi Azikiwe Da Ke Kaduna

by Alkazeem M. Shariff
2 months ago
Rayukan

Majiya mai tushe ta tabbatar da cewa daga karamar Salla zuwa yau an samu asarar rayuka akalla mutum 86 a babban titin Nnamdi Azikiwe da ke garin Kaduna, wanda aikin gyaran hanyar ya ki ci ya ki cinyewa.

A sakamakon aikin hanyar da ke tafiyar hawainiyya, akasarin wadanda suka rasa rayukansu, manyan motoci ne ke zama ajalinsu, kamar yadda wasu ganau, Dakta Muhammad Jamilu da Injiniya Muhammad Buhari, suka tabbatar mana da hakan.

Malam Muktar mai littafai Dan Mani, yana gudanar da ayyukansa kan babban titin, ya tabbatar da cewa irin abubuwa da ke faruwa a wannan babbar hanyar abin takaici ne, domin akwai ‘yan’uwansa da manyan motocin suka zama ajalinsu har lahira.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, shi ma wani Bawan Allah mai suna Alhaji Nasiru Wagini, wanda shi ma ya bayyana cewa, akwai danuwansa mai suna Dakta Hamza Wagini wanda kemist dinsa ke kasuwar barci Kaduna, shi ma daga zuwa isar da wani muhimmin sako wata babbar mota ta buga kansa da kankaren titin wanda ya yi sanadiyyar rasuwarsa.

A cewarsa, Alhaji Ado Baban Nazifi, mazaunin Unguwar Mu’azu Kaduna, shi ma daga zuwa kai kudin sadaki a Asukulaye kusa da masalacin Sheikh Dahiru Bauci, mota ta kashe shi har lahira.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Ya ce akwai wata mata da goyonta motar tirela ta takesu suka mutu a nan take, haka nan ma a ranar Lahadin da ta gabata, wata motar tirela ta sake halaka wani Bawan Allah mai suna Anas Abdulmumin Kura wanda aka fi sani da Albani, shi da dansa a daidai Kurmin Mashi kusa da sabuwar fanteka. 

Sai dai a kasantuwar rasa rayukan da ake yi a titin ya ta azzara sosai, hakan ya sa wasu mutane sun fara daukar doka a hannunsu, ta yadda wasu matasa ke kona mota da zaran hakan ya faru.

Jama’a da dama sun koka, inda suke kira ga mai girma Gwamna Jihar Kaduna, Malam Uba Sani da ya dube su da idon rahama ya dauki mataki, ya kuma ja hankalin gwamnatin tarayya da ta dauki mataki kawo karshen aikin wannan babbar hanyar, domin dakile cin rayukan al’umma da take yi.

Rayukan
Alkazeem M. Shariff
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnati Ta Amince Da A Dawo Da Tsofaffin Sojoji Fagen Daga

Matsalar Tsaro: Gwamnati Ta Amince Da A Dawo Da Tsofaffin Sojoji Fagen Daga

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.