ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rayukan Mutane Sama Da 86 Suka Salwanta A Kan Titin Nnamdi Azikiwe Da Ke Kaduna

by Alkazeem M. Shariff
3 months ago
Rayukan

Majiya mai tushe ta tabbatar da cewa daga karamar Salla zuwa yau an samu asarar rayuka akalla mutum 86 a babban titin Nnamdi Azikiwe da ke garin Kaduna, wanda aikin gyaran hanyar ya ki ci ya ki cinyewa.

A sakamakon aikin hanyar da ke tafiyar hawainiyya, akasarin wadanda suka rasa rayukansu, manyan motoci ne ke zama ajalinsu, kamar yadda wasu ganau, Dakta Muhammad Jamilu da Injiniya Muhammad Buhari, suka tabbatar mana da hakan.

Malam Muktar mai littafai Dan Mani, yana gudanar da ayyukansa kan babban titin, ya tabbatar da cewa irin abubuwa da ke faruwa a wannan babbar hanyar abin takaici ne, domin akwai ‘yan’uwansa da manyan motocin suka zama ajalinsu har lahira.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, shi ma wani Bawan Allah mai suna Alhaji Nasiru Wagini, wanda shi ma ya bayyana cewa, akwai danuwansa mai suna Dakta Hamza Wagini wanda kemist dinsa ke kasuwar barci Kaduna, shi ma daga zuwa isar da wani muhimmin sako wata babbar mota ta buga kansa da kankaren titin wanda ya yi sanadiyyar rasuwarsa.

A cewarsa, Alhaji Ado Baban Nazifi, mazaunin Unguwar Mu’azu Kaduna, shi ma daga zuwa kai kudin sadaki a Asukulaye kusa da masalacin Sheikh Dahiru Bauci, mota ta kashe shi har lahira.

LABARAI MASU NASABA

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Ya ce akwai wata mata da goyonta motar tirela ta takesu suka mutu a nan take, haka nan ma a ranar Lahadin da ta gabata, wata motar tirela ta sake halaka wani Bawan Allah mai suna Anas Abdulmumin Kura wanda aka fi sani da Albani, shi da dansa a daidai Kurmin Mashi kusa da sabuwar fanteka. 

Sai dai a kasantuwar rasa rayukan da ake yi a titin ya ta azzara sosai, hakan ya sa wasu mutane sun fara daukar doka a hannunsu, ta yadda wasu matasa ke kona mota da zaran hakan ya faru.

Jama’a da dama sun koka, inda suke kira ga mai girma Gwamna Jihar Kaduna, Malam Uba Sani da ya dube su da idon rahama ya dauki mataki, ya kuma ja hankalin gwamnatin tarayya da ta dauki mataki kawo karshen aikin wannan babbar hanyar, domin dakile cin rayukan al’umma da take yi.

Rayukan
Alkazeem M. Shariff
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

Rayukan
Labarai

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Ra'ayi Riga

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Rayukan
Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnati Ta Amince Da A Dawo Da Tsofaffin Sojoji Fagen Daga

Matsalar Tsaro: Gwamnati Ta Amince Da A Dawo Da Tsofaffin Sojoji Fagen Daga

LABARAI MASU NASABA

Rayukan

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Rayukan

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Rayukan

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
Rayukan

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.