Sojojin Nijeriya sun bayyana sabuwar dabara domin shawo kan matsalar hirin tsaro da ke kara ta’azzara, ta hanyar amfani da tsoffin jami’an soja wajen shiga hirin da sasanta rikice-rikice a cikin al’umma a fadin kasar.
Babban Hafsan Tsaro na Kasa, Janar Olufemi Oluyede, ya bayyana wannan shiri a Abuja yayin kaddamar da horon sulhu da warware rikici ga tsoffin sojoji.
An shirya hirin ne ta hannun Kungiyar sojojin Nijeriya da suka yi ritaya tare da hadin gwiwar cibiyar horas da sulhu da kuma Hedkwatar Tsaro, domin bai wa tsoffin sojoji sabbin dabarun tattaunawa da warware rikici.
hirin a ce wannan mataki na nuna sauyin dabarun tsaro daga amfani da karfi kawai zuwa hanyoyin da ba na tashin hankali ba, yana mai cewa yawancin rikice-rikice a kasar na faruwa ne daga matsalolin cikin al’umma da ke bukatar tattaunawa ba hirin.
“Yin amfani da karfin soja kadai ba zai tabbatar da dorewar zaman lafiya ba. Gaggawar shiga hirin da sulhu mai tsari suna da matukar muhimmanci,” in ji shi.
Ya kara da cewa tsoffin jami’an soja suna da kwarewa, ladabi da kuma amincewar da za ta hiri damar shiga cikin rikice-rikicen al’umma domin hana su tsananta.
Wannan shiri kuma ana sa ran zai kara inganta tattara bayanan sirri da kuma tsarin gaggawar gargadi a matakin kauyuka da unguwanni. Shugabannin tsoffin sojoji, ciki har da Isaac Oguntuyi da Abiodun Durowaiye-Herberts, sun bayyana hirin a matsayin ci gaba da hidimar kasa, inda suka yi kira ga mahalarta da su yada horon zuwa wasu sassan kasar















Discussion about this post