ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Bukaci N40m Kudin Fansar Yara 20 Da Suka Sace A Neja

by Sadiq
4 years ago
'Yan Bindiga

A halin yanzu ‘yan bindiga suna neman Naira miliyan 40 a matsayin kudin fansar yara 20 da suka yi garkuwa da su a Kusherki, karamar hukumar Rafi ta Jihar Neja. 

Mutanen da aka sace kimanin makonni uku da suka gabata, har yanzu suna hannun wadanda suka sace su.

  • Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya
  • El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

Alhaji Auwal Usman daga Kusherki ya bayyana cewa a halin yanzu ‘yan bindigar na neman Naira miliyan 40 kafin su sako yaran da suka yi garkuwa da su da ke fuskantar mawuyacin hali a hannun ‘yan bindigar.

ADVERTISEMENT

Wadanda aka yi garkuwa da su da suka hada da maza hudu da mata 16, dukkansu ‘yan shekaru hudu ne da kuma 10.

Usman ya yi kira da a kara himma da gwamnatin jihar da sauran masu ruwa da tsaki domin ganin an ceto su ba tare da wani ya samu rauni ba.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“Muna kira ga gwamnatin Jihar Neja da jami’an tsaro da su kawo mana dauki domin iyayen yaran da aka sace suna fuskantar matsananciyar matsin lamba sakamakon sace ‘ya’yansu,” in ji Usman.

A nasa jawabin kwamishinan tsaron cikin gida da ayyukan jin kai, Emmanuel Bagna Umar, ya bada tabbacin gwamnatin jihar ta kuduri aniyar kawar da duk wani nau’in laifuka a jihar.

Ya kara da cewa gwamnati na aiki tukuru tare da hadin gwiwar rundunonin kasa da kasa domin kubutar da yaran da sauran wadanda aka yi garkuwa da su a fadin jihar tare da tabbatar da cewa sun dawo wurin ‘yan uwansu a raye ba tare da an samu matsala ba.

Umar ya ci gaba da cewa: “Duk da cewa jihar na samun asarar rayuka, amma a gaskiya muna samun nasara a yakin da ake yi da ‘yan bindiga. Muna jinjina wa jami’an tsaro da kungiyoyin ‘yan banga a jihar kan yadda suke gudanar da ayyukansu.”

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Nacewa Ga Manufar Bude Kofa Yayin Da Take Raya Bangaren Makamashi

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Nacewa Ga Manufar Bude Kofa Yayin Da Take Raya Bangaren Makamashi

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.