An kashe Farfesa Gabriel Nyityo, malamin tarihi a Jami’ar Moses Orshio Adasu, da ke Makurd a Jihar Benuwai.
Wasu ’yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka harbe shi har lahira.
Majiyoyin tsaro sun ce an harbe Farfesan ne a gidansa da ke yankin Adaka, bayan layin masana’antu na Makurdi, da sanyin safiyar Laraba.
Wani malami a jami’ar ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana Farfesa Nyityo a matsayin mutum mai son zaman lafiya.
Ya ce mutuwarsa ta girgiza jama’a.
Tuni jama’a sun taru a gidan marigayin domin yi wa iyalansa ta’aziyya, yayin da aka kai gawarsa zuwa ɗakin ajiyar gawa.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, rundunar ’yansandan Jihar Benuwai ba ta fitar da sanarwa a hukumance kan lamarin ba.













