Sojojin rundunar Operation FANSAN YAMMA sun daƙile wasu shirye-shiryen kai hare-hare da ’yan bindiga ke yi tare da hallaka wani fitaccen kwamandan ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Kaura Namoda da ke Jihar Zamfara.
Rundunar sojin ta ce, bisa bayanan sirri da ta samu, dakarunta sun yi artabu da ’yan bindigan da ke shirin kai wa wasj yankuna hare-hare, inda suka tilasta musu ja da baya bayan musayar wuta.
A wani samame da aka kai a yankin Dogon Kade, sojojin sun hallaka Alhaji Tukur, wani kwamandan ’yan bindiga kuma ƙanin wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake nema ruwa a jallo, Alhaji Shehu Bagiwaye.
Wasu ’yan bindiga sun samu raunuka tare da tserewa zuwa dazuka.
A Sabon Gari ma, sojojin sun daƙile harin ’yan bindiga, inda suka kashe wani da ake zargin ɗan bindiga ne tare da ƙwato babur da ake zargin masu laifin sun yi amfani da shi.
Haka kuma, rundunar ta bayyana cewa jiragen saman yaƙin Nijeriya sun kai wa wasu ’yan bindiga kimanin 300 da ke kan babura hari yayin da suke tafiya zuwa yankin Bayazaki na kogin Gummi.
Rundunar ta ce harin ya yi sanadin raunata da kashe da dama daga cikinsu tare da daƙile wani babban shirinsu kai hari.













