ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 4 A Ekiti

by Sadiq
4 years ago
Matafiya

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu matafiya hudu a hanyar Ekiti zuwa Oke Ako a karamar hukumar Ajoni (LCDA) a Jihar Ekiti. 

An ce matafiyan na komawa Ibadan, babban birnin Oyo, bayan sun halarci wani taro a Jihar Kogi.

  • Yekuwar Kai Hare-Hare Abuja: British Airways Ya Dawo Da Jigilar Fasinja Zuwa Abuja
  • An Dakatar Da Mu Don Mun Nemi Mukamin Alkalin Babbar Kotun Kebbi – Wasu Alkalai

Wata majiya ta shaida wa NAN cewa an sace matafiya ne a ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

“Mutane hudun da aka sace suna dawowa ne daga wani taron da aka yi a Kogi zuwa Ibadan a kan hanyar Irele Ekiti da Oke Ako,” kamar yadda majiyar NAN ta ruwaito.

“Ba mu ji komai daga bakin ‘yan bindigar ba tun jiya kuma muna fatan za su tuntubi iyalansu, watakila don neman kudin fansa.”

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

A cewar NAN, Kehinde Abejide, shugaban al’ummar Irele-Ekiti, ya yi Allah-wadai da lamarin, ya kuma bukaci Biodun Oyebanji, gwamnan Ekiti da ya dauki matakan inganta tsaro a cikin al’umma.

“Wadannan mutane hudu suna komawa Ibadan ne lokacin da aka kai musu hari aka yi garkuwa da su da safiyar Lahadi, kuma ba mu ji komai ba tun lokacin da aka kwashe su zuwa,” in ji Abejide.

“Muna kuka muna rokon gwamnati ta taimaka mana a wannan yanki, amma ga dukkan alamu babu abin da ke faruwa, musamman idan aka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa a cikin al’umma.

“Ko da yake a baya mun yi shirye-shirye m a nan dangane da tsaro, amma a banza.

“Bari in yi kira ga gwamnan Ekiti da ya yi wani abu cikin gaggawa kan rashin tsaro kafin a halaka mutanenmu da daukacin al’ummar Ajoni LCDA.

“Akwai bukatar samar da wasu jami’an soja a tsakanin Irele da Oke Ako, wanda za su taimaka wajen dakile duk wani harin da ‘yan bindigar za su iya kai musu, domin da alama suna cin gajiyar rashin tsarin tsaro a nan.”

Sunday Abutu, kakakin ‘yansandan Ekiti, ya ce zai yi tsokaci kan lamarin idan ya samu karin bayani.

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.