ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 4 A Ekiti

by Sadiq
4 years ago
Matafiya

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu matafiya hudu a hanyar Ekiti zuwa Oke Ako a karamar hukumar Ajoni (LCDA) a Jihar Ekiti. 

An ce matafiyan na komawa Ibadan, babban birnin Oyo, bayan sun halarci wani taro a Jihar Kogi.

  • Yekuwar Kai Hare-Hare Abuja: British Airways Ya Dawo Da Jigilar Fasinja Zuwa Abuja
  • An Dakatar Da Mu Don Mun Nemi Mukamin Alkalin Babbar Kotun Kebbi – Wasu Alkalai

Wata majiya ta shaida wa NAN cewa an sace matafiya ne a ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

“Mutane hudun da aka sace suna dawowa ne daga wani taron da aka yi a Kogi zuwa Ibadan a kan hanyar Irele Ekiti da Oke Ako,” kamar yadda majiyar NAN ta ruwaito.

“Ba mu ji komai daga bakin ‘yan bindigar ba tun jiya kuma muna fatan za su tuntubi iyalansu, watakila don neman kudin fansa.”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

A cewar NAN, Kehinde Abejide, shugaban al’ummar Irele-Ekiti, ya yi Allah-wadai da lamarin, ya kuma bukaci Biodun Oyebanji, gwamnan Ekiti da ya dauki matakan inganta tsaro a cikin al’umma.

“Wadannan mutane hudu suna komawa Ibadan ne lokacin da aka kai musu hari aka yi garkuwa da su da safiyar Lahadi, kuma ba mu ji komai ba tun lokacin da aka kwashe su zuwa,” in ji Abejide.

“Muna kuka muna rokon gwamnati ta taimaka mana a wannan yanki, amma ga dukkan alamu babu abin da ke faruwa, musamman idan aka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa a cikin al’umma.

“Ko da yake a baya mun yi shirye-shirye m a nan dangane da tsaro, amma a banza.

“Bari in yi kira ga gwamnan Ekiti da ya yi wani abu cikin gaggawa kan rashin tsaro kafin a halaka mutanenmu da daukacin al’ummar Ajoni LCDA.

“Akwai bukatar samar da wasu jami’an soja a tsakanin Irele da Oke Ako, wanda za su taimaka wajen dakile duk wani harin da ‘yan bindigar za su iya kai musu, domin da alama suna cin gajiyar rashin tsarin tsaro a nan.”

Sunday Abutu, kakakin ‘yansandan Ekiti, ya ce zai yi tsokaci kan lamarin idan ya samu karin bayani.

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.