ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Kame Karin Mutum 7 ‘Yan Kungiyar Asiri A Edo

by Sadiq
4 years ago
Kungiyar Asiri

Rundunar ‘yan sandan jihar Edo a ranar Lahadi ta ce jami’anta sun kama wasu mutane bakwai da ake zargin ‘yan kungiyar asiri ne a jihar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimakiyar kakakin ‘yan sandan jihar, ASP Jennifer Iwegbu, wadda aka rabawa Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa (NAN) a Benin.

  • Ban Taba Umartar Kiristoci Su Sayi Bindiga Ba — Fasto Adeboye
  • PDP Reshen Jihar Osun Ta Koka Kan Yadda ‘Yan Sanda Ke Yi Wa ‘Ya’Yanta Dauki Dai-dai

NAN ta ruwaito cewa rundunar ‘yan sanda a ranar Juma’a ta kama tare da gabatar da ‘yan kungiyar asiri bakwai, wadanda ake zargin ‘yan kungiyar asiri ne na Eiye da Aiye.

ADVERTISEMENT

Iwegbu ta bayyana sunayen wadanda ake zargin Andrew Owhoyavwosa mai shekaru 22 da Joseph Meshak mai shekaru 25 da Osazee Solomon mai shekaru 35 da Godswill Obasohan mai shekaru 25 da Charles Odiase mai shekaru 52 da Okoh Peter mai shekaru 68.

An kama su ne a hannun Ekiadolor a cikin al’ummar Ekowe, yayin da na bakwai kuma an kama su ne a hanyar Igbe da ke karamar hukumar Auchi Etsako ta yammacin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A cewarta, an kama su ne kan irin kisan wuce gona da iri a jihar Edo da suke yi.

“A ranar 02/07/2022, jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Edo, reshen Ekiadolor, a yayin da suke sintiri a cikin garin Ekowe da kewaye, sun kama wasu da ake zargin ‘yan kungiyar asiri ne a gidan matasan unguwar.

“Wadanda ake zargin, da ganin jami’an ‘yan sandan, sun yi taho-mu-gama ne daga wajen taron da suka yi ba bisa ka’ida ba.

“Wannan matakin ya ja hankalin jami’an ‘yan sanda inda suka fatattake su wanda hakan ya sa aka kama mutanen shida.

“A wajen binciken da aka gudanar a wurin ya kai ga gano bindigogi guda biyu da aka kera a cikin gida, harsashi masu rai guda 30, akwatin bayar da agajin gaggawa guda daya, Kolanut, kwai, shanu, mushen kaza guda, wayoyin hannu da tsabar kudi Naira dubu talatin da bakwai,”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Jam’iyyar Labour Party Ba Za Ta Lashe Zaben 2023 Ba – Kwankwaso

Jam'iyyar Labour Party Ba Za Ta Lashe Zaben 2023 Ba - Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.