Wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun sake kai hari mai muni a wani sansanin sojoji da ke ƙauyen Kemanji, ƙaramar hukumar Kaiama a Jihar Kwara, inda suka kashe sojoji uku.
Rahotanni sun ce harin ya faru ne a safiyar ranar Litinin da asuba, inda aka ji ƙarar harbe-harbe mai ƙarfi a yankin.
Maharan sun kai farmaki mamaya ne sansanin sojojin, inda suka fafata da jami’an tsaro a wani mummunan artabu wanda ya jawo asarar rayuka a ɓangaren sojoji.
Wani mazaunin yankin da ya buƙaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa lamarin ya zo ba zato ba tsammani, yana mai tabbatar da cewa sojoji uku sun rasa rayukansu a harin.
Ya ce, “Wasu daga cikin sojojin suna barci ma da misalin ƙarfe 3 na dare lokacin da ‘yan ta’addan suka kutsa cikin sansanin suka kashe uku daga cikinsu kafin sauran sojojin su mayar da martanin wuta”.
Har yanzu ba a san adadin waɗanda aka kashe a ɓangaren maharan ba, yayin da hukumomin tsaro har yanzu ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba game da lamarin.















Discussion about this post