Jami’an Rundunar ‘Yansandan Nijeriya a Jihar Kogi sun ceto ɗaliban makarantar Islamiyya 17 da aka sace a Lokoja, yayin da hukumomin tsaro ke ƙara ƙaimi domin ceto sauran waɗanda har yanzu suke hannun masu garkuwa da mutanen.
An sace ɗaliban ne a ranar 26 ga Afrilu da misalin ƙarfe 11:45 na dare lokacin da wasu ‘yan bindiga suka mamaye makarantar Daarul Kitab School, wata makarantar Islamiyya mai haɗe da gidan marayu da ke yankin Zariagi a kan hanyar NNPC Road, Kabba Junction.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Saliu Afusat, ya bayyana a wata sanarwa cewa, mutane 26 ne aka sace, ciki har da ɗalibai 24 da mata biyu na mamallakin makarantar.
Afusat ya ce bayan aukuwar lamarin, jami’in ‘yansanda mai kula da yankin B Division Lokoja ya tattara tawagar haɗin gwiwar jami’an tsaro, wanda hakan ya kai ga ceto mutane 17 daga cikin waɗanda aka sace.















Discussion about this post