Rundunar ’yansandan jihar Zamfara ta ceto mutane uku da ake zargin ’yan bindiga ne suka yi garkuwa da su, tare da sake gargadin jama’a kan biyan kudin fansa ga masu aikata laifuka a wani bangare na kokarin dakile matsalar garkuwa da mutane a jihar.
Da yake tabbatar da lamarin, jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya ce an ceto mutanen ne yayin sintiri da ayyukan gina amincewar jama’a da aka gudanar a yankunan da ke fuskantar barazanar tsaro a jihar.
Ya ce aikin, wanda aka gudanar ranar 31 ga Mayu, 2026, da misalin karfe 1:00 na rana, ya hada da hadin gwiwar tawagar tsaro da ta kunshi rundunar sintirin babura, jami’an rundunar ’yansanda ta musamman ta 42 PMF, sashen yaki da manyan laifuka na VCRU, da kuma jami’an kare al’umma na jihar (CPG).
A cewarsa, tawagar ta samu nasarar ceto mutanen ne a yankin dajin Bingi da ke karamar hukumar Maru yayin gudanar da sintiri na yau da kullum domin karfafa tsaro da dawo da kwarin gwiwar jama’a.
An bayyana sunayen wadanda aka ceto da Yusuf Ibrahim mai shekaru 15, Basiru Yusuf mai shekaru 17, da Mubarak Ibrahim mai shekaru 18.















Discussion about this post