An kammala taron tattaunawa na Shangri-La karo na 23 a kasar Singapore kwanan nan. A cikin wa’adin taron mai kwanaki uku, an ga ra’ayoyi 2 masu sabani da juna.
A gefe guda, wakilan Sin sun yi bayani game da ra’ayin Sin kan tsarin shugabancin duniya da kuma manufar tsaro, bisa kalubalen tsaro da duniya ke fuskanta a yau, inda ta isar da sakon kiyaye zaman lafiya da inganta hadin gwiwa a duniya, wanda ya samu karbuwa sosai.
A gefe guda kuma, wakilan Japan sun yi yunkurin neman hujja kan ayyukansu na “sake daukar makamai da karfin soja”, wakilan Philippines kuma sun dasa ayar tambaya kan ma’anar tsai da “ka’idojin tafiyar da harkoki a tekun kudancin Sin”, kuma dukkansu sun fuskanci suka daga bangarori daban-daban.
Wasu ’yan fashin baki suna ganin cewa, a wannan taron, muryar Sin ta fi karfi sosai, wadda ba wai kawai ta shafi yanayin taron ba, har ma ta zama ingantaccen karfi mai samar da kwanciyar hankali da tabbaci ga duk fadin duniya da ke fuskantar rikice-rikice.
Daga gabatar da manyan shawarwari guda hudu na tafiyar da harkokin duniya, zuwa kokarin raya dangantakar da ke tsakanin manyan kasashe don tabbatar da samun zaman karko bisa manyan tsare-tsare, har zuwa bayyana ra’ayin kin nuna kasaita da fin karfi da tabbatar da aminci da adalci a dandalolin duniya, kasar Sin ta riga ta zama ginshikin tabbatar da zaman lafiya da na karko a yankin Asiya da tekun Fasifik, har ma a duk fadin duniya.
Babu shakka, za a kara fahimtar yadda ya kamata wata babbar kasa ta sauke nauyin da ke wuyanta a gun taron tsaro na tattaunawa na Shangri-La na bana. (Amina Xu Kande Gao)














Discussion about this post