A yau Litinin, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana cewa kasar Sin ta yi imanin yarjejeniyar hana bazuwar makaman nukiliya ta NPT, ita ce ginshikin burin sassan kasa da kasa na kwance damara da hana bazuwar makaman nukiliya.Mao ta ce, NPT ta kasance muhimmin ginshiki na wanzar da tsaron kasa da kasa bayan yakin duniya na 2.
Jami’ar ta bayyana hakan ne yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, yayin da take tsokaci game da wasu rahotanni masu bayyana yadda aka gaza cimma nasarar amincewa da kundin karshe, na taro karo na 11 na nazari game da yarjejeniyar ta NPT, lamarin da aka danganta da sabanin dake tsakanin Amurka da Iran.
Mao, wadda ta yi furucin yayin da aka nemi ta yi tsokaci game da yiwuwar Amurka da Iran su cimma matsaya, ta ce har kullum kasar Sin na da imanin cewa, tattaunawa da gudanar da shawarwari su ne hanya daya tilo ta warware batun kasar Iran, kuma amfani da karfin tuwo ba abun da zai haifar illa mummunan sakamako. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post