ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

by Sulaiman
3 weeks ago

Attajirin da ya fi kowa arziki a Afirka, Aliko Dangote, kwanan nan ya halarci wata tattaunawa ta podcast mai suna ‘In Good Company’.

Tattaunawar ta fi mayar da hankali kan jarin da Dangote ke zubawa, amma yanayin tambayoyin da amsoshin da ya bayar, sai suka yi kama da irin waɗanda mai neman aiki ke bayarwa.

Tabbas ba neman aiki yake yi ba. An kiyasta arzikin Dangote ya kai kusan dala biliyan 30, kuma a cikin tattaunawar ya bayyana shirinsa na zuba jarin fiye da dala biliyan 45 a nahiyar Afirka.

ADVERTISEMENT

Amma shirin ‘In Good Company’, babbar nasara ce ga Dangote saboda kasancewar shirin, ya fi mayar da hankali ne kan manyan ’yan kasuwa, shugabannin duniya da fitattun masu tunani.

Dangote ya burge mai gabatar da shirin, Nicolai Tangen, da kwarin gwiwarsa da kuma shirinsa na zuba makudan kudade a Afirka, ciki har da gina daya daga cikin manyan cibiyoyin masana’antu a nahiyar — matatar mai ta dala biliyan 20 mai karfin tace ganga 650,000 a rana.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Dangote ya nuna kwarewarsa sosai yayin tattaunawar, inda ya yi magana kan ladabi a kasuwanci, muhimmancin hangen nesa da kuma fahimtar bukatun kasuwannin Afirka.

A cewarsa, daya daga cikin manyan bukatun nahiyar shi ne samar da siminti, wanda kasashen Afirka da dama ke fama da karancinsa. Ya ambaci Nijeriya, Zambia da Congo Brazzaville a matsayin kasashen da suke zaman jira har watanni uku kafin su samu siminti.

Da aka tambaye shi inda ya samo kudin gina matatar mai, Dangote ya bayyana bayanai fiye da yadda ya saba yi. Game da bambance-bambancen al’adun kamfanoni a Afirka da wahalar gudanar da kasuwanci, Dangote bai raina nahiyar ba.

Maimakon haka, ya fi mayar da hankali kan al’adun aiki a cikin kamfanoni daban-daban da kuma matakin horas da ma’aikata, wanda ya ce za su iya yin nasara a duk inda suka shiga a fadin duniya.

Dangote har ya ambaci makarantar horaswa da kamfaninsa ke gudanarwa domin zakakuran dalibai daga jami’o’in Nijeriya da sauran kasashen Afirka.

Nicolai Tangen, ba kawai mai gabatar da podcast ba ne; shi ne babban jami’in gudanarwa na ‘Norges Bank Investment Management’, wanda ke kula da Asusun Arzikin Kasa na Norway.

Asusun na Norway shi ne mafi girman asusun gwamnati na zuba jari a duniya, inda yake da kadarori da suka haura dala tiriliyan 2.

Yana da hannun jari a kamfanoni 7,200 a kasashe 70 na duniya.Tattaunawar podcast din da Dangote ya yi wani bangare ne na tattaunawa da hadin gwiwar asusun domin zuba jari a Dangote da kuma Afirka baki daya.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

MASU ALAKA

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi
Labarai

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

June 29, 2026
Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina
Labarai

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha
Manyan Labarai

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
Next Post
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

June 29, 2026
Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.