ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

by Sulaiman
20 seconds ago

Attajirin da ya fi kowa arziki a Afirka, Aliko Dangote, kwanan nan ya halarci wata tattaunawa ta podcast mai suna ‘In Good Company’.

Tattaunawar ta fi mayar da hankali kan jarin da Dangote ke zubawa, amma yanayin tambayoyin da amsoshin da ya bayar, sai suka yi kama da irin waɗanda mai neman aiki ke bayarwa.

Tabbas ba neman aiki yake yi ba. An kiyasta arzikin Dangote ya kai kusan dala biliyan 30, kuma a cikin tattaunawar ya bayyana shirinsa na zuba jarin fiye da dala biliyan 45 a nahiyar Afirka.

ADVERTISEMENT

Amma shirin ‘In Good Company’, babbar nasara ce ga Dangote saboda kasancewar shirin, ya fi mayar da hankali ne kan manyan ’yan kasuwa, shugabannin duniya da fitattun masu tunani.

Dangote ya burge mai gabatar da shirin, Nicolai Tangen, da kwarin gwiwarsa da kuma shirinsa na zuba makudan kudade a Afirka, ciki har da gina daya daga cikin manyan cibiyoyin masana’antu a nahiyar — matatar mai ta dala biliyan 20 mai karfin tace ganga 650,000 a rana.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Dangote ya nuna kwarewarsa sosai yayin tattaunawar, inda ya yi magana kan ladabi a kasuwanci, muhimmancin hangen nesa da kuma fahimtar bukatun kasuwannin Afirka.

A cewarsa, daya daga cikin manyan bukatun nahiyar shi ne samar da siminti, wanda kasashen Afirka da dama ke fama da karancinsa. Ya ambaci Nijeriya, Zambia da Congo Brazzaville a matsayin kasashen da suke zaman jira har watanni uku kafin su samu siminti.

Da aka tambaye shi inda ya samo kudin gina matatar mai, Dangote ya bayyana bayanai fiye da yadda ya saba yi. Game da bambance-bambancen al’adun kamfanoni a Afirka da wahalar gudanar da kasuwanci, Dangote bai raina nahiyar ba.

Maimakon haka, ya fi mayar da hankali kan al’adun aiki a cikin kamfanoni daban-daban da kuma matakin horas da ma’aikata, wanda ya ce za su iya yin nasara a duk inda suka shiga a fadin duniya.

Dangote har ya ambaci makarantar horaswa da kamfaninsa ke gudanarwa domin zakakuran dalibai daga jami’o’in Nijeriya da sauran kasashen Afirka.

Nicolai Tangen, ba kawai mai gabatar da podcast ba ne; shi ne babban jami’in gudanarwa na ‘Norges Bank Investment Management’, wanda ke kula da Asusun Arzikin Kasa na Norway.

Asusun na Norway shi ne mafi girman asusun gwamnati na zuba jari a duniya, inda yake da kadarori da suka haura dala tiriliyan 2.

Yana da hannun jari a kamfanoni 7,200 a kasashe 70 na duniya.Tattaunawar podcast din da Dangote ya yi wani bangare ne na tattaunawa da hadin gwiwar asusun domin zuba jari a Dangote da kuma Afirka baki daya.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
Manyan Labarai

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta
Manyan Labarai

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

June 8, 2026
Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.