Bayan samun goyon bayan Gwamnan Jihar Gombe, an amince da Jamilu Isyaku Gwamna, a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a watan da ya gabata.
Yanzu a babban zaɓen 2027 Gwamna zai fafata da Bala Tinka na jam’iyyar ADC, da kuma Isa Pantami na jam’iyyar PDP, wanda dukkansu -Tinka da Pantami, sun koma sabbin jam’iyyunsu ne bayan sun gaza samun tikitin takara a APC.
Yayin da yake sanar da Gwamna a matsayin ɗan takarar APC, Gwamna Inuwa Yahaya, ya bayyana shi a matsayin gogaggen ɗan siyasa kuma ƙwararren ma’aikacin gwamnati da ke da karɓuwa a tsakanin al’umma, wanda a cewarsa Gwamna yana da amana da kuma tasirin da zai tabbatar wa jam’iyyar nasara a zaɓe mai zuwa.
Da yake nuna godiyarsa kan wannan amana, Jamilu Gwamna, ya yi alƙawarin ci gaba da ɗora wa kan nasarorin da gwamnatin Jihar Gombe ta samu tare da ɗaga martabar jihar zuwa wani sabon matsayi na ci gaba.
Samun tikitin jam’iyyar APC mai mulki wani muhimmin sauyi ne a tafiyar siyasar Gwamna, wanda tun a shekarar 2007 ya fara neman kujerar gwamnan jihar Gombe ƙarƙashin jam’iyyar ANPP.
A lokacin yaƙin neman zaɓensa na 2007, Gwamna ya ziyarci shalkwatar Kamfanin LEADERSHIP Group, inda ya bayyana burinsa da hangen nesansa na ci gaban Jihar Gombe.
Shekaru kusan ashirin kenan yana jiran wannan dama inda samun tikitin jam’iyyar mai mulki, wanda bai taɓa samu a baya ba, ya kusantar da shi ga cikar burinsa na zama gwamna, abin da ma sunansa “Gwamna” ke nuni da shi.
A shekarar 2011, ya shaida yadda ɗan uwansa, Ibrahim Dankwambo, ya bar aikin gwamnati a matakin tarayya tare da samun tikitin PDP, wanda ya kai shi ga zama gwamnan jihar.
Bayan shekaru takwas, yanayin siyasa bai ba da damar wani ɗan uwa ya gaji wani a kujerar gwamna ba amma daga bisani, a shekarar 2022, bayan ya kasa samun tikitin PDP, Jamilu Gwamna ya fice daga jam’iyyar tare da mara wa wa’adin mulki na biyu na Gwamna Inuwa Yahaya baya.
A wancan lokaci ma, Gwamna ya soki PDP, yana mai cewa jam’iyyar ba ta shirya karɓar mulki ba inda aka rawaito shi yana cewa; “A gare ni wannan mataki shawara ce ta kaina, tun da ban shirya yin ritaya daga siyasa ba, dole na nemi wata hanya, kuma wannan hanyar ita ce komawa APC.”
Duk da haka, ya jaddada cewa goyon bayan da ya bai wa Inuwa Yahaya, ba don wata buƙata ta kansa ba ne, sai dai saboda ci gaban jihar da kuma imaninsa cewa gwamnan na gudanar da aiki mai kyau kuma zai iya yin fiye da haka.
Yanzu alamu na nuna cewa wannan amincewa da goyon bayan da ya bai wa Gwamna Inuwa Yahaya, sun fara haifar masa da ɗa mai ido, domin gwamnan ya nuna masa irin wannan karamci ta hanyar mara masa baya domin samun tikitin takarar gwamna.














Discussion about this post