ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

by Sulaiman and Naziru Adam Ibrahim
3 weeks ago
Jamilu Gwamna

Bayan samun goyon bayan Gwamnan Jihar Gombe, an amince da Jamilu Isyaku Gwamna, a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a watan da ya gabata.

Yanzu a babban zaɓen 2027 Gwamna zai fafata da Bala Tinka na jam’iyyar ADC, da kuma Isa Pantami na jam’iyyar PDP, wanda dukkansu -Tinka da Pantami, sun koma sabbin jam’iyyunsu ne bayan sun gaza samun tikitin takara a APC.

Yayin da yake sanar da Gwamna a matsayin ɗan takarar APC, Gwamna Inuwa Yahaya, ya bayyana shi a matsayin gogaggen ɗan siyasa kuma ƙwararren ma’aikacin gwamnati da ke da karɓuwa a tsakanin al’umma, wanda a cewarsa Gwamna yana da amana da kuma tasirin da zai tabbatar wa jam’iyyar nasara a zaɓe mai zuwa.

ADVERTISEMENT

Da yake nuna godiyarsa kan wannan amana, Jamilu Gwamna, ya yi alƙawarin ci gaba da ɗora wa kan nasarorin da gwamnatin Jihar Gombe ta samu tare da ɗaga martabar jihar zuwa wani sabon matsayi na ci gaba.

Samun tikitin jam’iyyar APC mai mulki wani muhimmin sauyi ne a tafiyar siyasar Gwamna, wanda tun a shekarar 2007 ya fara neman kujerar gwamnan jihar Gombe ƙarƙashin jam’iyyar ANPP.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

A lokacin yaƙin neman zaɓensa na 2007, Gwamna ya ziyarci shalkwatar Kamfanin LEADERSHIP Group, inda ya bayyana burinsa da hangen nesansa na ci gaban Jihar Gombe.

Shekaru kusan ashirin kenan yana jiran wannan dama inda samun tikitin jam’iyyar mai mulki, wanda bai taɓa samu a baya ba, ya kusantar da shi ga cikar burinsa na zama gwamna, abin da ma sunansa “Gwamna” ke nuni da shi.

A shekarar 2011, ya shaida yadda ɗan uwansa, Ibrahim Dankwambo, ya bar aikin gwamnati a matakin tarayya tare da samun tikitin PDP, wanda ya kai shi ga zama gwamnan jihar.

Bayan shekaru takwas, yanayin siyasa bai ba da damar wani ɗan uwa ya gaji wani a kujerar gwamna ba amma daga bisani, a shekarar 2022, bayan ya kasa samun tikitin PDP, Jamilu Gwamna ya fice daga jam’iyyar tare da mara wa wa’adin mulki na biyu na Gwamna Inuwa Yahaya baya.

A wancan lokaci ma, Gwamna ya soki PDP, yana mai cewa jam’iyyar ba ta shirya karɓar mulki ba inda aka rawaito shi yana cewa; “A gare ni wannan mataki shawara ce ta kaina, tun da ban shirya yin ritaya daga siyasa ba, dole na nemi wata hanya, kuma wannan hanyar ita ce komawa APC.”

Duk da haka, ya jaddada cewa goyon bayan da ya bai wa Inuwa Yahaya, ba don wata buƙata ta kansa ba ne, sai dai saboda ci gaban jihar da kuma imaninsa cewa gwamnan na gudanar da aiki mai kyau kuma zai iya yin fiye da haka.

Yanzu alamu na nuna cewa wannan amincewa da goyon bayan da ya bai wa Gwamna Inuwa Yahaya, sun fara haifar masa da ɗa mai ido, domin gwamnan ya nuna masa irin wannan karamci ta hanyar mara masa baya domin samun tikitin takarar gwamna.

Jamilu Gwamna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    NDLEA Ta Lalata Kilo12,234 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sulaiman
    Majalisa Ta Yi Tsit Yayin Da Gwamnati Ke Keta Haddin Amso Bashi – Sarkin Sanusi II
  • Sulaiman
    Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela
  • Sulaiman
    Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma
Jamilu Gwamna
Naziru Adam Ibrahim
+ posts Bio
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Shugaba Tinubu Ya Isa Nairobi Domin Halartar Taron Tattalin Arzikin Nahiyar Afirka
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Gwamnatin Filato Ta Kwato Kadarorin Jihar Da Aka Wawashe

MASU ALAKA

Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa
Siyasa

Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa

June 29, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP
Siyasa

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Manyan Labarai

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Next Post
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Lalata Kilo12,234 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 29, 2026
CBN

Majalisa Ta Yi Tsit Yayin Da Gwamnati Ke Keta Haddin Amso Bashi – Sarkin Sanusi II

June 29, 2026
Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

June 29, 2026
Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

June 29, 2026
Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

June 29, 2026
Yadda Yara Suka Kamo Harsasan Harbo Jirgin Sama A Yayin Kamun Kifi A Borno

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Ɗaliban NECO A Borno

June 29, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Da Philippines Na Keta Hakkoki Da Muradunta Na Teku

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Da Philippines Na Keta Hakkoki Da Muradunta Na Teku

June 29, 2026
Xi Jinping Zai Bayar Da Lambar Yabo Ta Ranar 1 Ga Watan Yuli Tare Da Gabatar Da Jawabi Albarkacin Cikar JKS Shekaru 105 Da Kafuwa

Xi Jinping Zai Bayar Da Lambar Yabo Ta Ranar 1 Ga Watan Yuli Tare Da Gabatar Da Jawabi Albarkacin Cikar JKS Shekaru 105 Da Kafuwa

June 29, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Far Wa Makaranta, Sun Sace Ɗaliban NECO A Borno

Ƴan Ta’adda Sun Far Wa Makaranta, Sun Sace Ɗaliban NECO A Borno

June 29, 2026
Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa

Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa

June 29, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.