Hukumar EFCC na shirin gurfanar da shugaban Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Abdullahi Bodejo, a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan zargin safarar kuɗi da ya kai kusan dala miliyan 2.53 da kuma ɗaukar nauyin ta’addanci.
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawar ta shigar da tuhume-tuhume guda 12 a kansa, inda take zarginsa da karɓar maƙudan kuɗaɗe da dala a tsabar kuɗi ba tare da amfani da wata cibiyar kuɗi kamar yadda doka ta tanada ba.
A cewar EFCC, ana zargin Bodejo ya karɓi wasu kuɗaɗe daga tsohon Akanta-Janar na Jihar Bauchi, Sa’idu Abubakar, tsakanin 2022 da 2024.
Kuɗaɗen da ake zargin ya karɓa sun haɗa da dala 100,000, dala 200,000, dala 500,000 da kuma dala 980,000, da sauran wasu kuɗaɗe.
Har ila yau, hukumar ta zarge shi da mallakar kuɗaɗen da ake zargin sun samo asali ne daga haramtattun ayyuka.
EFCC ta ce laifukan da ake zarginsa da aikatawa sun saɓa wa dokokin hana almundahana na Nijeriya kuma doka ta tanadi hukunci a kansu.
Ana sa ran za a gurfanar da Bodejo a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja da zarar kotun ta sanya ranar sauraron shari’ar.














