Shekaru 80 da suka gabata, alkalin Sin da ya halarci shari’o’in Tokyo Mei Ruao ya yi kashedin cewa, manta wahalhalun baya zai haifar da hadari a nan gaba.
Bayan shekaru 80, kasar Japan ta sake farfado da sabon ra’ayin nuna karfin soja, ana iya ganin daraja da ma’anar shari’o’in Tokyo a tarihi.
A ranar 3 ga watan Mayun shekarar 1946, biyo bayan tanade-tanaden mika wuya da Japan ta yi ba tare da wani sharadi ba da kuma na kotun hukunta laifukan yakin duniya na II da kasashen kawance suka gabatar, kotun ta fara sauraron shari’a kan laifukan yakin, kuma bisa haduwar manyan kasashe 11 da hujjoji da shaidu masu karfi da aka gabatar, wadannan shari’o’i sun samu sojojin Japan da laifin kaddamar da yaki da take dokokin kasa da kasa da bayyana irin ta’asar da Japanawa suka aikata a kasashen Asiya da dama.
An kuma yanke wa manyan masu laifi su 25 hukuncin kisa ta hanyar rataya ko zaman gida yari, cikinsu har da Hideki Tojo. Haka kuma an karyata shari’o’i kamar “shari’ar tabbatar da nasara” da “yakin Japan na kare kai” da “dokar gyara hukunce-hukunce.”Bayan shekaru 80, an samu babban sauyi a yanayin duniya. A halin yanzu, gwamnatin Takaichi Sanae ta kasar Japan ta gaggauta raya sabon ra’ayin nuna karfin soja, wanda ya kawo barazana ga odar duniya.
Japan ta dauki matakai sannu a hankali don yada ra’ayin karfafa karfin soja, kamar su daga kasafin kudin tsaron kasa, da amincewa da fitar da manyan makamai, da gaggauta jibge makamai, da goyon bayan mallakar makaman nukiliya, da sa kaimi ga gyara ka’idoji uku na tsaron kasa, da shiryawa yaki na dogon lokaci, wadanda dukkansu suka jawo hankalin kasa da kasa.Ma’aikatar harkokin wajen Rasha ta bayyana cewa, shari’o’in Tokyo, mataki ne mai muhimmanci a fannin kare doka da kuma tarihin bil’adama baki daya.
Ta ce ba a kayyade tsawon lokacin bincike da yanke hukunci kan laifuffukan da sojojin Japan suka aikata a yakin duniya na biyu na cin zarafin bil’adama ba, hakan ya sa za a ci gaba da bincike kan wadannan laifuka. (Zainab Zhang)















Discussion about this post