Jam’iyyar APC ta sanar da tsawaita wa’adin sayar da fom ɗin tsayawa takara, tare da ƙara wa’adin miƙa su, a wani mataki na bai wa masu neman takara damar kammala shirye-shiryensu gabanin zaɓen 2027.
A cikin wata sanarwar manema labarai da sakataren yaɗa labarai na ƙasa, Felix Morka, ya sanya wa hannu, jam’iyyar ta ce an tsawaita sayar da fom ɗin zuwa ƙarfe 12 na dare na ranar Laraba, 6 ga Mayu, 2026, yayin da aka ƙara wa’adin miƙa fom ɗin da aka cike zuwa ranar Alhamis, 7 ga Mayu, 2026.
Haka kuma, APC ta bayyana cewa za a gudanar da tantance ’yan takara daga ranar Juma’a, 8 ga Mayu zuwa Talata, 12 ga Mayu, 2026, kafin fitar da sunayen waɗanda suka yi nasarar tsallake matakin a ranar Laraba, 13 ga Mayu, 2026.
Jam’iyyar ta bayyana cewa sauye-sauyen na daga cikin matakan da ake ɗauka domin tabbatar da gaskiya da adalci a tsarin zaɓen cikin gida, tare da bai wa dukkan masu sha’awar takara dama iri daya.
Masu lura da harkokin siyasa na ganin cewa wannan mataki na APC zai ƙara ƙarfafa shirin jam’iyyar gabanin babban zaɓen 2027, musamman ganin yawan masu neman takara a matakai daban-daban.















Discussion about this post