ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

by Sadiq
1 year ago
APC

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta ce za ta ɗauki matakin shari’a kan jam’iyyar PDP saboda zargin da ta yi wa Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle, da hannu a satar mutane a jihar.

Mai magana da yawun jam’iyyar APC, Yusuf Idris Gusau, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

  • Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki
  • An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC

A cewarsa, zargin da Mustapha Jafaru Kaura, mai magana da yawun Gwamna Dauda Lawal, ya yi, ba su da tushe, siyasa ce kawai.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta fito ne bayan taron gaggawa da kwamitin aiki na jam’iyyar APC a jihar ya gudanar karkashin jagorancin Hon. Tukur Umar Danfulani, inda suka tattauna batun wata hira da Kaura ya yi a wani bidiyo da aka yaɗa a yanar gizo.

A hirar, Kaura ya yi iƙirarin cewa satar ɗaliban makarantar sakandare ta Kankara a Jihar Katsina da aka yi a ranar 11 ga watan Disamban 2020, an tsara ta ne da sanin Matawalle.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Haka kuma, ya zargi Matawalle da karɓar Naira miliyan 300 daga tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari, don a sako ɗaliban, amma ya bai wa ‘yan bindiga miliyan 30 kacal.

APC ta ƙaryata wannan zargi.

Ta kuma bayyana cewa zargin Kaura yana shafar wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar kamar tsohon Gwamna Abdulaziz Yari, wanda yanzu ke wakiltar Zamfara ta Yamma a Majalisar Dattawa.

Jam’iyyar APC ta ƙalubalanci Kaura da ya kawo hujjoji kan wannan zargi da kuma wasu mutane da aka sace a jihar, kamar satar ɗalibai mata 270 daga makarantar Government Girls Secondary School da ke Jangebe a ranar 26 ga watan Fabrairun 2021, da kuma satar ɗaliban Kwalejin Noma da Kiwo da ke Bakura.

APC ta jaddada cewa gwamnatin Matawalle ta yi ƙoƙari wajen yaƙi da ‘yan bindiga da ceto al’ummomi da dama.

Ta bayyana yankuna kamar Gwaram, Kanoma, Kaya, Faru, Janbako, Lilo da Anka, a matsayin wuraren da aka gudanar da ayyukan tsaro da taimako.

Jam’iyyar ta kuma ce tana duba yiwuwar ɗaukar matakin shari’a kan gidan talabijin na Maibiredi TV da ya watsa hirar da ake ganin an shirya don ɓata sunan ministan.

Ta zargi PDP da ƙoƙarin karkatar da hankalin jama’a daga gazawarta ta hanyar yaɗa ƙarya da tayar da fitina don samun moriyar siyasa.

A ƙarshe, APC ta yi kira ga mambobinta da su zauna lafiya da bin doka, inda ta bayar da tabbacin cewa gaskiya za ta fito fili, kuma za a yi adalci.

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
Siyasa

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Next Post
Ya Kamata Ana Kammala Shari’ar Zaɓe Kafin Rantsuwa

Ya Kamata Ana Kammala Shari'ar Zaɓe Kafin Rantsuwa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.