Babbar Kotun Jihar Kano ta ɗage shari’ar tsohon Gwamnan Jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da matarsa Hafsat Umar, da kuma wasu mutum shida zuwa ranar 14 ga watan Oktoba, 2026. An gurfanar da Ganduje ne tare da sauran waɗanda ake tuhuma kan zargi guda 11 da suka haɗa da cin hanci, da haɗin baki, da almundahana, da kuma karkatar da kuɗaɗen gwamnati da suka kai biliyoyin naira a lokacin da yake gwamna.
Sauran waɗanda ake ƙara a cikin wannan shari’ar sun haɗa da Abubakar Bawuro, da Abdullahi Umar, da Jibrilla Muhammad, da wasu kamfanoni guda uku da suka haɗa da Lamash Properties Ltd, da Safari Textiles Ltd, da kuma Lasage General Enterprises Ltd. Lokacin da aka dawo zaman kotun domin sauraron hujjoji da buƙatun da ke gaban kotun, lauyan gwamnati ya nemi izinin janye wata buƙata ta da can domin maye gurbinta da sabuwa.
Lauyan mai gabatar da ƙara, Mista Victor Oni, ya sanar da kotu cewa jihar a shirye take ta ci gaba da shari’ar, inda ya shigar da sabuwar buƙata ta ranar 15 ga watan Mayu, 2026, a matsayin martani ga lauyan wanda ake ƙara na shida ya shigar na neman a dakatar da shari’ar. Lauyoyin sauran waɗanda ake ƙara sun bayyana cewa su ma a shirye suke su ci gaba da fuskantar shari’ar.
Sakamakon haka, mai shari’a Amina Adamu-Aliyu ta soke tsohuwar buƙatar mai gabatar da ƙara, sannan ta ɗege zaman kotun zuwa ranar 14 ga watan Oktoba domin sauraron abin da lauyan wanda ake ƙara na shida ya shigar. Wannan shari’a tana ɗaya daga cikin manyan shari’un da ke ɗaukar hankalin al’ummar Jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya saboda nauyin zargin da ake yi wa tsohon gwamnan.














