Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya halarci taron tattaunawa da wakilan ‘yan kasuwa mahalarta dandalin tattaunawar tattalin arzikin duniya na bazara ko DAVOS na shekarar 2026, a birnin Dalian na lardin Liaoning dake arewa maso gabashin kasar Sin. Rahotanni sun ce, wakilan ‘yan kasuwa kusan 150 daga sama da kasashe da yankunan duniya 30 ne suka halarci tattaunawar.
Bayan sauraron tsokaci daga wakilan, Li ya ce, bude kofa da hadin gwiwa su ne hanyoyin da ba za a iya kawarwa a zamanin da ake ciki ba, kana su ne abubuwan da kasashen duniya ke bukata domin fadada ci gabansu.Ya ce, ko wadanne irin sauye-sauye da aka fuskanta daga waje, Sin za ta ci gaba da bin turbar tarihi ta bude kofa da hadin gwiwa, da zurfafa shiga harkokin kasa da kasa na cinikayya da zuba jari, da ingiza hade sassa daban daban, da dunkule kasuwarta da kasuwannin kasa da kasa.
Har ila yau, firaministan na Sin ya ce, kasarsa za ta rarraba gajiyar kasuwarta ta cikin gida da sauran sassan duniya, kuma a shirye take ta shigo da hajoji masu inganci daga dukkanin kasashen duniya, da goyon bayan daidaiton bunkasar cinikayya tare da sauran sassa. (Saminu Alhassan)














