Kwamitin Kula da Asusun Jama’a na Majalisar Dattawa ya bayar da umarnin kama tsohon Babban Daraktan Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL), Mele Kyari, saboda rashin halartar zaman binciken da ake yi kan zargin karkatar da kudade har Naira tiriliyan 210 tsakanin shekarun 2017 zuwa 2023.
An dauki wannan matakin ne bayan Kyari ya ci gaba da kin bayyana a gaban kwamitin da ke gudanar da bincike kan tambayoyin da Ofishin Babban Mai Binciken Kudi na Tarayya ya yi dangane da bayanan kudin kamfanin.
Sai dai tsohon Babban Jami’in Kudi na NNPCL, Umar Isa, ya kalubalanci zargin a gaban kwamitin, yana mai cewa babu wasu kudade da suka ɓace.Ya kuma bayyana cewa adadin Naira tiriliyan 210 da ake magana a kai yana iya rikitar da jama’a idan aka kwatanta shi da hakikanin kudaden shiga da kamfanin ya samu a lokacin.
An bayar da umarnin kama Kyari ne bayan ’yan majalisar sun yi watsi da bukatar kara jinkirta binciken, tare da dagewa cewa dole ne a ci gaba da gudanar da binciken ba tare da ɓata lokaci ba.














Discussion about this post