A jiya Talata ne aka bude taron dandalin tattauna hadin gwiwar fasahohi da masana’antun aikin gona na Sin da Afirka na kwanaki 3 a birnin Nairobin kasar Kenya. A yayin taron, wakilai sama da 100 daga hukumomin gwamnatin Sin da na kasashen Afirka, da kungiyoyin kasa da kasa, da cibiyoyin nazarin kimiyya da fasaha, da manyan makarantu, da kungiyoyin kasuwanci, da kuma kamfanoni da dama, sun yi tattaunawa mai zurfi kan sabuwar hanyar habaka hadin gwiwar Sin da Afirka, a fannin neman zamanintar da aikin gona cikin hadin gwiwa.
Jakadiyar kasar Sin dake kasar Kenya, Guo Haiyan ta gabatar da jawabi a yayin bikin kaddamar da taron, inda ta ce bisa tsarin taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, zamanintar da aikin gona ya kasance muhimmin bangare a hadin gwiwar Sin da Afirka domin cimma moriyar juna.
Kasashen Afirka na da albarkatun kasa da matasa masu yawa, kuma idan har aka hade fasahohin neman ci gaba na kasar Sin, da fasahohin aikin gona na zamani, da kuma manyan kasuwanni na kasar Sin, tabbas za su bayar da muhimmiyar gudummawa a fannin gaggauta zamanintarwar aikin gona, da daga matsayin samar da isasshen hatsi, da neman wadata tare a kasar Sin da kasashen Afirka.
A nasa tsokaci kuwa, mataimakin shugaban shirin raya noma ta hanyar jure sauyin yanayi na Afirka ko AGRA mista Hamadi Boga, ya bayyana cewa, hadin gwiwar aikin gona zai samar da damammaki ga kasar Sin da kasashen Afirka wajen kafa tsarin samar da isasshen hatsi mai inganci, da samar da guraben aikin yi tare da kuma samun wadata tare.
An gudanar da taron na wannan karo ne karkashin hadin gwiwar cibiyar kirkire-kirkiren kimiyya da fasahar aikin gona ta Jingwa, da kwalejin nazarin tattalin arziki da manufofin abinci ta duniya dake jami’ar aikin gona ta kasar Sin, da kawancen shirin AGRA, da kuma taron kirkire-kirkiren kimiyya da fasahar aikin gona na duniya da dai sauransu. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post