ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Taron Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Fasahohi Da Masana’antun Aikin Gona na Sin Da Afirka A Kenya

by Sulaiman
53 minutes ago
Kenya

A jiya Talata ne aka bude taron dandalin tattauna hadin gwiwar fasahohi da masana’antun aikin gona na Sin da Afirka na kwanaki 3 a birnin Nairobin kasar Kenya. A yayin taron, wakilai sama da 100 daga hukumomin gwamnatin Sin da na kasashen Afirka, da kungiyoyin kasa da kasa, da cibiyoyin nazarin kimiyya da fasaha, da manyan makarantu, da kungiyoyin kasuwanci, da kuma kamfanoni da dama, sun yi tattaunawa mai zurfi kan sabuwar hanyar habaka hadin gwiwar Sin da Afirka, a fannin neman zamanintar da aikin gona cikin hadin gwiwa.

Jakadiyar kasar Sin dake kasar Kenya, Guo Haiyan ta gabatar da jawabi a yayin bikin kaddamar da taron, inda ta ce bisa tsarin taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, zamanintar da aikin gona ya kasance muhimmin bangare a hadin gwiwar Sin da Afirka domin cimma moriyar juna.

Kasashen Afirka na da albarkatun kasa da matasa masu yawa, kuma idan har aka hade fasahohin neman ci gaba na kasar Sin, da fasahohin aikin gona na zamani, da kuma manyan kasuwanni na kasar Sin, tabbas za su bayar da muhimmiyar gudummawa a fannin gaggauta zamanintarwar aikin gona, da daga matsayin samar da isasshen hatsi, da neman wadata tare a kasar Sin da kasashen Afirka.

ADVERTISEMENT

A nasa tsokaci kuwa, mataimakin shugaban shirin raya noma ta hanyar jure sauyin yanayi na Afirka ko AGRA mista Hamadi Boga, ya bayyana cewa, hadin gwiwar aikin gona zai samar da damammaki ga kasar Sin da kasashen Afirka wajen kafa tsarin samar da isasshen hatsi mai inganci, da samar da guraben aikin yi tare da kuma samun wadata tare.

An gudanar da taron na wannan karo ne karkashin hadin gwiwar cibiyar kirkire-kirkiren kimiyya da fasahar aikin gona ta Jingwa, da kwalejin nazarin tattalin arziki da manufofin abinci ta duniya dake jami’ar aikin gona ta kasar Sin, da kawancen shirin AGRA, da kuma taron kirkire-kirkiren kimiyya da fasahar aikin gona na duniya da dai sauransu. (Mai Fassara: Maryam Yang)

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

Kenya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa
  • Sulaiman
    Zargin Sace Naira Tiriliyan 210: Majalisa Ta Bayar da Umarnin Kama Tsohon Shugaban NNPC, Mele Kyari
  • Sulaiman
    Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su
  • Sulaiman
    An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

MASU ALAKA

Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su

June 10, 2026
Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?
Daga Birnin Sin

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

June 10, 2026
An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Next Post
Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

June 10, 2026
An Kaddamar Da Taron Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Fasahohi Da Masana’antun Aikin Gona na Sin Da Afirka A Kenya

An Kaddamar Da Taron Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Fasahohi Da Masana’antun Aikin Gona na Sin Da Afirka A Kenya

June 10, 2026
NNPCL

Zargin Sace Naira Tiriliyan 210: Majalisa Ta Bayar da Umarnin Kama Tsohon Shugaban NNPC, Mele Kyari

June 10, 2026
Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su

Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su

June 10, 2026
An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

June 10, 2026
Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

June 10, 2026
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026
An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

June 10, 2026
An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.