ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyayar Shugaban Faransa A Kasar Sin Karin Dama Ce Ta Yaukaka Ci Gaban Turai Da Duniya Baki Daya

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Faransa

Yayin da shugaban Faransa Emmanuel Macron ke gudanar da ziyarar aiki yanzu haka a kasar Sin, masharhanta da dama na ganin wannan ziyara wadda ita ce irinta ta hudu da yake gudanarwa a Sin, ta wuce batun raya huldar diflomasiyya kadai, domin kuwa ziyarar za ta samar da wani zarafi mai kima, da damammaki masu tasirin gaske ga Turai, a fannin bunkasa kirkire-kirkire da jagorancin duniya. Yayin da ake ganin sauye-sauyen al’amuran duniya cikin sauri, bai kamata sashen Turai ya bari a bar shi a baya ba.

Tuni dai kasar Sin ta zamo babbar cibiyar tattalin arziki da fasahohin zamani a duniya. Ga kasashen Turai, ciki har da Faransa, lokaci ya yi da za su gaggauta hade kamfanoninsu da sassan da su ne makomar gobe a fannin raya tattalin arziki. Misalin wadannan sassa sun hada da na raya ababen hawa masu tashi kusa da doron duniya, da masu amfani da makamashi mai tsafta, da fannin raya birane, da kere-keren mutum-mutumin inji zuwa fasahar kirkirarriyar basira ta AI.

Shugaba Macron na da damar ingiza karsashin Turai, da tabbatar da nahiyar ta zamo abokiyar tafiya, ba wai kawai kasuwa shigar da hajoji ba. Tafiyar hawainiya a wannan fanni na iya haifarwa Turai matukar koma baya, musamman a gabar nan da Sin, tare da sauran kasashe masu samun saurin bunkasa ke da tasirin kara mamaye makomar duniya a gwamman shekaru masu zuwa.

ADVERTISEMENT

A ganina wannan ziyara da shugaban Faransa ke yi yanzu haka a kasar Sin, kamata ya yi ta zamo damar kara azamar tsara matakan hadin gwiwa da Sin, ta yadda Faransa za ta ingiza tsarin raya nahiyar Turai daga fannoni daban daban. Domin kuwa, a yayin da duniya ke samun saurin sauyin fasahohin zamani, babu zabin yin jinkiri, wajibi ne a gaggauta shiga tafiyar neman ci gaba tare.

Tabbas hadakar tafiya tsakanin Sin da Turai ta shallake batun samun moriyar tattalin arziki kadai. Ya kamata ziyarar shugaba Macron ta wannan karo ta gaggauta sauya tsarin jagorancin mabambantan sassan duniya ta yadda Sin da Turai za su samu karin zarafi na raya kansu tare.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Ko shakka babu, wannan ziyara ta shugaba Macron dama ce da ba kasafai a kan same ta ba, don haka ya wajaba a yi himmar cin gajiyarta. Lokaci ne da ya kamata Faransa da Turai su shigar da kansu muhimmin dandalin kirkire-kirkire da jagorancin duniya, domin kaucewa zama ’yan kallo a nan gaba. (Saminu Alhassan)

Faransa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Faransa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Next Post
Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bai Wa Nakasassu 250 Tallafi A Zamfara

Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bai Wa Nakasassu 250 Tallafi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.