Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya miƙa cak na kuɗi da ya kai Naira biliyan 5.81 domin biyan bashin garatutin ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya da kuma iyalan ma’aikatan da suka rasu.
Gwamnan ya gabatar da cak ɗin ne jiya a zauren Majalisar Zartarwa da ke Gidan Gwamnatin Maiduguri, tare da halartar shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago da na Ƙungiyar ‘Yan Fansho, a wani mataki na inganta jin daɗin ma’aikatan da suka yi ritaya da kuma iyalan ma’aikatan da suka rasu.
A matsayin wani ɓangare na ƙudirin gwamnatinsa na biyan haƙƙoƙin ma’aikata, Zulum ya tuna cewa gwamnatinsa na fitar da Naira miliyan 200 duk wata domin biyan garatuti. Haka kuma, ta fitar da Naira biliyan 8 domin biyan haƙƙoƙin masu karɓar fansho da garatutin malamai a shekarar 2025, yayin da a shekarar 2020 ta ware Naira biliyan 12 domin biyan kusan ma’aikatan gwamnati na jiha da ƙananan hukumomi 5,000 da suka yi ritaya.
Gwamnan ya bayyana cewa cak na farko, wanda ya kai Naira 2,992,301,964.95, zai biya dukkan bashin garatutin da ake bin iyalan ma’aikatan gwamnati da suka rasu.
Ya ce cak na biyu, wanda ya kai Naira 2,822,528,306.99, zai biya garatutin duk masu ritaya har zuwa watan Disambar 2022, tare da haɗa da bashin ma’aikatan Ma’aikatar Gidaje ta Borno daga shekarar 2013 zuwa yanzu.
A nasa jawabin, Kwamishinan Kuɗi na jihar, Lawan Umar Dalorima, ya yabawa Gwamna Zulum bisa jajircewarsa wajen kula da jin daɗin ma’aikata da masu ritaya.
Dalorima ya ce biyan kuɗaɗen na nuna ƙudirin gwamnatin jihar na girmama waɗanda suka sadaukar da mafi kyawun shekarun rayuwarsu wajen yi wa Jihar Borno hidima.














