ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

by Sulaiman
2 months ago
Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya miƙa cak na kuɗi da ya kai Naira biliyan 5.81 domin biyan bashin garatutin ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya da kuma iyalan ma’aikatan da suka rasu.

Gwamnan ya gabatar da cak ɗin ne jiya a zauren Majalisar Zartarwa da ke Gidan Gwamnatin Maiduguri, tare da halartar shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago da na Ƙungiyar ‘Yan Fansho, a wani mataki na inganta jin daɗin ma’aikatan da suka yi ritaya da kuma iyalan ma’aikatan da suka rasu.

A matsayin wani ɓangare na ƙudirin gwamnatinsa na biyan haƙƙoƙin ma’aikata, Zulum ya tuna cewa gwamnatinsa na fitar da Naira miliyan 200 duk wata domin biyan garatuti. Haka kuma, ta fitar da Naira biliyan 8 domin biyan haƙƙoƙin masu karɓar fansho da garatutin malamai a shekarar 2025, yayin da a shekarar 2020 ta ware Naira biliyan 12 domin biyan kusan ma’aikatan gwamnati na jiha da ƙananan hukumomi 5,000 da suka yi ritaya.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya bayyana cewa cak na farko, wanda ya kai Naira 2,992,301,964.95, zai biya dukkan bashin garatutin da ake bin iyalan ma’aikatan gwamnati da suka rasu.

Ya ce cak na biyu, wanda ya kai Naira 2,822,528,306.99, zai biya garatutin duk masu ritaya har zuwa watan Disambar 2022, tare da haɗa da bashin ma’aikatan Ma’aikatar Gidaje ta Borno daga shekarar 2013 zuwa yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

A nasa jawabin, Kwamishinan Kuɗi na jihar, Lawan Umar Dalorima, ya yabawa Gwamna Zulum bisa jajircewarsa wajen kula da jin daɗin ma’aikata da masu ritaya.

Dalorima ya ce biyan kuɗaɗen na nuna ƙudirin gwamnatin jihar na girmama waɗanda suka sadaukar da mafi kyawun shekarun rayuwarsu wajen yi wa Jihar Borno hidima.

Zulum
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang
  • Sulaiman
    Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris
  • Sulaiman
    Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu
  • Sulaiman
    Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Labarai

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Zulum
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Zulum
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Next Post
Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Zulum

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Zulum

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Zulum

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.