ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

by Sadiq
2 months ago
Hamas

Tun da farko kan mambobin kwamitin zaben ya rabu kan wanda zai zama sabon shugaban kungiyar.

A zagayen farko na zaben ba a samu wanda ya yi nasara kai tsaye ba.

A cewar wani jami’in Falasdinawa mai masaniya kan zaben, tsohon shugaban ofishin siyasa na Hamas, Khaled Mashaal, ya samu kuri’u fiye da Al-Hayya, amma bai kai adadin kuri’un da ake bukata domin samun nasara kai tsaye ba.

ADVERTISEMENT

Bisa ga dokokin Hamas, dole ne dan takara ya samu akalla kuri’u 36 daga kwamitin zaben mai mambobi 69.

An fahimci cewa zagaye na biyu na zaben ne ya tantance wanda ya yi nasara.

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

Wane ne Khalil al-Hayya?

An haifi Khalil al-Hayya ranar 5 ga watan Nuwamban 1960.

Ya samu digirinsa na farko a jami’ar Musulunci da ke Gaza, yayin da ya samu digirinsa na biyu a Jami’ar Jordan.

Sannan ya samu digirin digirgir a jami’ar Kur’ani da ilimin Addinin Musulunci.

Ya shiga Hamas ne bayan kammala digirinsa na farko a lokacin yana aiki a matsayin malamin makaranta.

Ya rike mukamai a kungiyar har zuwa matsayin babban mataimakin sashen siyasar kungiyar, mukamin da ya rike har zuwa Agustan 2024.

Al-Hayya, wanda a baya ya kasance jagoran kungiyar Hamas a kasashen waje, ana kallonsa cikin masu tsattsauran ra’ayi a Hamas, wanda ya fito fili a lokacin yakin Isra’ila da Hamas da ya fara kusan shekaru uku da suka gabata.

Ana daukarsa a matsayin daya daga cikin amintattun mutane na kusa ga tsohon shugaban Hamas, Yahya Sinwar, kuma an bayyana shi a matsayin “daya daga cikin tsirarun mutanen da Sinwar yake ji da su.”

Bayan kashe Yahya Sinwar a watan Oktoban 2024, an rika kallon Al Hayya a matsayin daya daga cikin wadanda za su iya maye gurbinsa a shugabancin kungiyar.

Wace rawa ya taka a Hamas?

A matsayinsa na babban mai shiga tsakani a tattaunawar Hamas, al-Hayya ya samu karbuwa a idon duniya ta hanyar jagorantar tawagogin kungiyar a tattaunawar tsagaita wuta, inda ya rika ganawa da masu shiga tsakani daga Masar da Katar.

A baya-bayan nan ya kasance babban jami’in diplomasiyyar da tsare-tsare siyasar.

A watan Nuwamban 2019, Al Hayya da Rouhi Mushtaha suka jagoranci wata tawaga daga Gaza, zuwa kasashe da dama, ciki har da Turkiyya da Lebanon.

Al Hayya ya kuma jagoranci tattaunawar sulhu da kungiyar Fatah.

A watan Janairun 2022, ya ziyarci Aljeriya bayan ya samu gayyata daga shugaban kasar Aljeriya.

Al Hayya ya wakilci Hamas a tattaunawar da aka yi da Isra’ila kan sakin mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su da kuma tsagaita wuta.

Ya sha tsallake rijiya da baya

A watan Satumban 2025, Al-Hayya mai shekara 65 ya tsallake rijiya da baya a wani hari da Isra’ila ta kai kan shugabannin Hamas da ke wani taro a Doha, babban birnin Katar.

A lokacin harin an kashe mutum biyar ciki har da dansa, wanda mamba ne a rundunar tsaron Katar.

A lokacin, Firaministan Isra’ila ya ce an kai musu harin ne saboda zarginsu da kitsa harin ranar 7 ga watan Oktoban 2023 a kudancin Isra’ila, wanda ya haifar da yakin Gaza.

Da fari an kashe wasu ‘ya’yan Al-Hayya biyu a wani hari da aka kai da nufin halaka shi a Gaza, yayin da aka kashe dansa na hudu a wani hari a Gaza cikin watan Mayun da ya gabata.

A 2007 ne wani harin Isra’ila kan gidansa ya kashe bakwai daga cikin ‘yan’uwansa, ciki har da shakikansa biyu.

Haka ma a 2008 aka kashe daya daga cikin ‘ya’yansa a wani hari ta sama da aka kai masa.

Sannan a 2014 aka kashe wani dan nasa da surukarsa da kuma jikansa a wani hari ta sama

MASU ALAKA

Hamas
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Hamas
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
Hamas
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.