ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

by Sani Anwar
38 minutes ago
Magarya

Itaciyar magarya na da dimbin tarihi yadda ya kamata, sannan tana maganin abubuwa masu daman gaske da suka hada da cutukan daji, ciwon miki (idan wani tsiro ko kari ya fitowa mutum a jikinsa).

Idan aka samu ganyen magarya aka busar da shi, sai a daka a tankade shi sosai. Don haka, ga mai ciwon gyambo ko kuma wanda yake da ciwon da ya ki warkewa, har ake tunanin ko shafar sa aka yi ko kuma wani abu daban aka yi masa, kamar sihiri da sauran makamantansa, sai a nemi wannan ganye na magarya a yi amfani da shi.

Da farko dai, za a nemi ruwan dumi a tafasa shi sosai; sai a samu garin ganyen magaryar a zuba a ciki, bayan ya dan huce sai a wanke ciwon da shi. Bayan wanke ciwon, sai kuma a kawo garin magaryar tankadadde a zuba a kan ciwon ko gyambon, wanda ya ki ci ya ki cinyewa; daga nan in sha Allahu za a samu waraka.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, ana yin maganin sihiri da ganyen magarya, ma’ana; ga duk wanda ake tunanin an yi masa sihiri, sai a nemo ganyen magarya guda bakwai a mutsittshika su, domin kuwa sihiri ya kasu kashi bakwai, akwai wanda ake raba mutum da mutum, akwai wanda ake sa wa mutum cuta ya rika yawan kwanciya, akwai wanda ake kashe wa mutum kasuwa, akwai kuma wanda ake sa wa mutum rashin lafiya da sauran makamantansu.

Saboda haka, da zarar an fahimci an yi wa mutum daya daga cikin wadannan sihiri, a samo ganyen magarya guda bakwai a murje su da hannu, a zuba a ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

Daga nan kuma, akwai ayoyin alkur’ani da ake bukatar a tofa a cikin wannan ruwa, wanda ya hada da suratul a’arafi aya ta dari da sha bakwai zuwa aya ta dari da ashirin da biyu, sai suratul Yunus aya ta saba’in da tara zuwa aya ta tamanin da biyu.

Haka nan kuma, suratul Daha aya ta sittin da biyu zuwa ta saba’in. Daga nan, za a tofa Falaki da Nasi da Ayatul kursiyyu a ciki. Kazalika, za a karanta Kulya ayyuhal kafiruna a tofa a cikin ruwan da aka zuba wannan ganyen magarya, sai a ba wa wanda ake tunanin an yi wa wannan sihiri ya sha, ragowar ruwan kuma sai ya shafe jikinsa baki-daya; za a samu waraka da yardar Allah.

Magarya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

MASU ALAKA

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
Kiwon Lafiya

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kiwon Lafiya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

July 25, 2026
Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

July 25, 2026
Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

July 25, 2026
Magarya

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Magarya

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Magarya

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.