Gwamnatin Tarayya ta ce ƙalubalen tsaro da Nijeriya ke fuskanta a yanzu ba shi da wata nasaba da addini, sai dai ta nanata cewa, ana yin duk mai yiwuwa don magance ta’addanci da duk wani nau’in tsattsauran ra’ayi mai tayar da hankali a fadin kasar.
Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Yarima Lateef Fagbemi (SAN), ya bayyana hakan a ranar Talata a Abuja yayin da yake jawabi ga manema labarai bayan wani taron sirri da dan Majalisar Dokokin Amurka da Jakadan Amurka a Nijeriya, Richard Mills Jr.
In ba a manta ba, mun rahoto a kwanakin baya cewa, Shugaban Amurka, Donald Trump, a watan Oktoba, ya ayyana Nijeriya a matsayin ‘kasa mai kalubale na musamman’ a martanin da ya mayar kan zargin kisan kiyashin Kirista a kasar.
Trump, a cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, ya bayyana cewa, “Kiristanci na fuskantar barazanar wanzuwa a Nijeriya. Ana kashe dubban Kiristoci. Masu tsattsauran ra’ayi ne ke da alhakin wannan kisan kiyashin. Don haka, na sanya Nijeriya ta zama cikin jerin ‘kasashe masu matsala ta musamman’.”














