Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya yi kakkausan martani ga kalaman kuskure na wasu kasashe dangane da batun tekun kudancin kasar Sin, yayin jawabin da ya yi a jiya Litinin 8 ga watan nan.
A jawabin na Sun, mai taken “Tekuna da dokar teku”, yayin zama na 80 na babban zauren MDD, ya jaddada cikakken ikon mallakar da Sin ke da shi kan tsibiran dake kewayen tekun kudancin kasar da sassan ruwa dake kewayensu, kana da ikon mallaka na dukkanin sassan ruwa masu nasaba da batun. Ya ce ikon mulkin yankuna da hakkokin Sin kan sassan tekun kudancin kasar na da goyon bayan tabbataccen tushe na tarihi da doka.
Jami’in ya kara da cewa, akwai yanayin daidaito a halin da ake ciki yanzu haka a yankin tekun kudancin Sin. Amma Amurka na ci gaba da karfafa matakan jibge sojoji da ayyukansu a tekun kudancin Sin, tana ingizawa, da rura wutar tashin hankali da sabani, wanda hakan shi ne babban kalubale a yankin.
Don haka ne kasar Sin ke nacewa matsayinta na warware dukkanin sabani ta hanyar tattaunawa, da gudanar da shawarwari tare da kasashen da kai tsaye lamarin ya shafa, tana kuma aiwatar da cikakkun yarjeniyoyi masu nasaba da yankin tare da kasashe membobin kungiyar ASEAN, tare da ingiza gudanar da shawarwari kan hakan, da hada karfi wajen wanzar da zaman lafiya da daidaito a yankin tekun kudancin Sin, da goya baya ga ci gaba da walwala a shiyyarta. (Saminu Alhassan)














