Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta rahotannin da ke yawo a shafukan sada zumunta cewa yana shirin shirya zanga-zanga kan taɓarɓarewar matsalar tsaro a kasar nan.
Kwankwaso ya bayyana zarge-zargen a matsayin karya da yaudara, tare da bukatar ’yan Nijeriya su yi watsi da rahotannin, wanda ya ce an kirkiro su ne domin haddasa rudani da kuma karkatar da hankulan jama’a domin ribar siyasa.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Litinin, tsohon gwamnan jihar Kano ya ce shi ko jam’iyyar NDC ba sa goyon bayan duk wani abu da zai iya kawo tarnaki ga zaman lafiya ko haddasa karya doka da oda.
Ya bukaci jama’a su rika tantance gaskiyar bayanai kafin yada su, musamman a kafafen sada zumunta inda labaran karya ke yaduwa cikin sauri.
Yayin da ya sake jaddada kudirinsa na gudanar da siyasa cikin lumana, Kwankwaso ya ce zai ci gaba da fafutukar siyasar da ta mayar da hankali kan batutuwa masu muhimmanci da kuma tattaunawa mai amfani yayin da kasar ke shirin babban zabe mai zuwa.















Discussion about this post