ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe

by Sani Anwar
3 weeks ago
Amince

Majalisar zartaswa ta tarayya (FEC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta amince da inganta cibiyar kula da saran maciji da ke garin Kaltungo a Jihar Gwambe zuwa “Cibiyar binciken cizon maciji ta ƙasa Kaltungo, a jihar ta Gombe.”

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate ne ya bayyana hakan, bayan taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC), a ranar Litinin da ta gabata.

Da yake yi wa manema labarai jawabi bayan taron, Ministan ya ce; majalisar zartarwa ta tarayya, ta yi la’akari da wasu muhimman abubuwa guda huɗu da suka shafi lafiyar ƴan Nijeriya tare da amince da haka.

ADVERTISEMENT

Pate ya ce, na farko shi ne; inganta cibiyar kula da saran maciji da ke Kaltungo a Jihar Gwambe zuwa cibiyar bincike da kula da cizon maciji ta ƙasa tare da faɗaɗa aikin kula da lafiya, horar da bincike don amsa buƙatu da kuma ba da kulawa mai kyau ga waɗanda maciji ya farwa.

Ministan ya lura cewa, cizon maciji ya kasance wani babban ƙalubalen kiwon lafiyar jama’a, musamman a yankunan karkara, kuma yana da matuƙar wahala ga masu rauni, manoma, makiyaya, mafarauta, mata da yara, waɗanda rayuwarsu da ayyukansu na yau da kullun, za su iya kai wa ga haɗuwa da maciji.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Ya ce, amincewar ta zama dole, saboda saran macizai na haifar da mutuwa, tawaya da raunin tunani tare da munanan yanayi na zamantakewa.

A cewarsa, “Wannan sabuwar cibiya, za ta kasance wata muhimmiyar cibiya da za ta tunkari ƙalubalen, musamman a shiyyar Arewa-maso-gabas da Arewa-maso-yamma, da kuma shiyyar Arewa-ta-tsakiya ta Nijeriya, inda lamarin ya fi ƙamari.

“Sabuwar cibiyar, za ta samar da cikakkiyar kulawa ta musamman ga saran maciji da sauran batutuwan da suka shafi gudanar da bincike a kan cututtukan da suka shafi maciji, rigakafi, tantancewa da magani, tabbatar da samun ci gaba mai ɗorewa da samar da ingantaccen maganin dafin maciji da kuma samun cikakken sashin asibiti da na likitanci, domin inganta kula da majinyata da ayyukan ƙwararru da sauran makamantansu.

“Haka zalika kuma, za ta yi haɗin gwiwa da cibiyoyin ƙasa da ƙasa. Wannan babban mataki ne da ya kawo wata cibiya da za ta kasance irinta ta farko a faɗin ƙasar nan, amma kuma a yankinmu.”

Pate ya kuma ce, abu na biyu shi ne; amincewa da sayen motocin asibiti guda 10 da ke ba da gudummawar jini, domin ayyukan shiyya na hukumar kula da jini ta ƙasa, don sauƙaƙa saye, tara da rarraba jini a kowace shiyya.

Ya ce, Nijeriya na buƙatar gudummawar jini kimanin miliyan 1.8 a duk shekara, inda ya ƙara da cewa; a halin yanzu, ƙasar na samun kusan kashi 25 zuwa 30 ne kacal.

“Za a iya tura waɗannan motoci na ba da gudummawar jini, don tara masu ba da gudummawa, ta yadda za mu inganta tarin jini mai muhimmanci ga mata masu juna biyu, ga waɗanda suka ji rauni da waɗanda aka yi wa tiyata ko kuma ga waɗanda ake yi wa tiyata, amma kuma ga waɗanda ake jinyar cutar daji, waɗanda ke buƙatar ƙarin jini ko wasu abubuwa na jini.

Amince
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.