Majalisar zartaswa ta tarayya (FEC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta amince da inganta cibiyar kula da saran maciji da ke garin Kaltungo a Jihar Gwambe zuwa “Cibiyar binciken cizon maciji ta ƙasa Kaltungo, a jihar ta Gombe.”
Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate ne ya bayyana hakan, bayan taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC), a ranar Litinin da ta gabata.
Da yake yi wa manema labarai jawabi bayan taron, Ministan ya ce; majalisar zartarwa ta tarayya, ta yi la’akari da wasu muhimman abubuwa guda huɗu da suka shafi lafiyar ƴan Nijeriya tare da amince da haka.
Pate ya ce, na farko shi ne; inganta cibiyar kula da saran maciji da ke Kaltungo a Jihar Gwambe zuwa cibiyar bincike da kula da cizon maciji ta ƙasa tare da faɗaɗa aikin kula da lafiya, horar da bincike don amsa buƙatu da kuma ba da kulawa mai kyau ga waɗanda maciji ya farwa.
Ministan ya lura cewa, cizon maciji ya kasance wani babban ƙalubalen kiwon lafiyar jama’a, musamman a yankunan karkara, kuma yana da matuƙar wahala ga masu rauni, manoma, makiyaya, mafarauta, mata da yara, waɗanda rayuwarsu da ayyukansu na yau da kullun, za su iya kai wa ga haɗuwa da maciji.
Ya ce, amincewar ta zama dole, saboda saran macizai na haifar da mutuwa, tawaya da raunin tunani tare da munanan yanayi na zamantakewa.
A cewarsa, “Wannan sabuwar cibiya, za ta kasance wata muhimmiyar cibiya da za ta tunkari ƙalubalen, musamman a shiyyar Arewa-maso-gabas da Arewa-maso-yamma, da kuma shiyyar Arewa-ta-tsakiya ta Nijeriya, inda lamarin ya fi ƙamari.
“Sabuwar cibiyar, za ta samar da cikakkiyar kulawa ta musamman ga saran maciji da sauran batutuwan da suka shafi gudanar da bincike a kan cututtukan da suka shafi maciji, rigakafi, tantancewa da magani, tabbatar da samun ci gaba mai ɗorewa da samar da ingantaccen maganin dafin maciji da kuma samun cikakken sashin asibiti da na likitanci, domin inganta kula da majinyata da ayyukan ƙwararru da sauran makamantansu.
“Haka zalika kuma, za ta yi haɗin gwiwa da cibiyoyin ƙasa da ƙasa. Wannan babban mataki ne da ya kawo wata cibiya da za ta kasance irinta ta farko a faɗin ƙasar nan, amma kuma a yankinmu.”
Pate ya kuma ce, abu na biyu shi ne; amincewa da sayen motocin asibiti guda 10 da ke ba da gudummawar jini, domin ayyukan shiyya na hukumar kula da jini ta ƙasa, don sauƙaƙa saye, tara da rarraba jini a kowace shiyya.
Ya ce, Nijeriya na buƙatar gudummawar jini kimanin miliyan 1.8 a duk shekara, inda ya ƙara da cewa; a halin yanzu, ƙasar na samun kusan kashi 25 zuwa 30 ne kacal.
“Za a iya tura waɗannan motoci na ba da gudummawar jini, don tara masu ba da gudummawa, ta yadda za mu inganta tarin jini mai muhimmanci ga mata masu juna biyu, ga waɗanda suka ji rauni da waɗanda aka yi wa tiyata ko kuma ga waɗanda ake yi wa tiyata, amma kuma ga waɗanda ake jinyar cutar daji, waɗanda ke buƙatar ƙarin jini ko wasu abubuwa na jini.














