ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe

by Sani Anwar
1 day ago
Amince

Majalisar zartaswa ta tarayya (FEC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta amince da inganta cibiyar kula da saran maciji da ke garin Kaltungo a Jihar Gwambe zuwa “Cibiyar binciken cizon maciji ta ƙasa Kaltungo, a jihar ta Gombe.”

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate ne ya bayyana hakan, bayan taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC), a ranar Litinin da ta gabata.

Da yake yi wa manema labarai jawabi bayan taron, Ministan ya ce; majalisar zartarwa ta tarayya, ta yi la’akari da wasu muhimman abubuwa guda huɗu da suka shafi lafiyar ƴan Nijeriya tare da amince da haka.

ADVERTISEMENT

Pate ya ce, na farko shi ne; inganta cibiyar kula da saran maciji da ke Kaltungo a Jihar Gwambe zuwa cibiyar bincike da kula da cizon maciji ta ƙasa tare da faɗaɗa aikin kula da lafiya, horar da bincike don amsa buƙatu da kuma ba da kulawa mai kyau ga waɗanda maciji ya farwa.

Ministan ya lura cewa, cizon maciji ya kasance wani babban ƙalubalen kiwon lafiyar jama’a, musamman a yankunan karkara, kuma yana da matuƙar wahala ga masu rauni, manoma, makiyaya, mafarauta, mata da yara, waɗanda rayuwarsu da ayyukansu na yau da kullun, za su iya kai wa ga haɗuwa da maciji.

LABARAI MASU NASABA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Ya ce, amincewar ta zama dole, saboda saran macizai na haifar da mutuwa, tawaya da raunin tunani tare da munanan yanayi na zamantakewa.

A cewarsa, “Wannan sabuwar cibiya, za ta kasance wata muhimmiyar cibiya da za ta tunkari ƙalubalen, musamman a shiyyar Arewa-maso-gabas da Arewa-maso-yamma, da kuma shiyyar Arewa-ta-tsakiya ta Nijeriya, inda lamarin ya fi ƙamari.

“Sabuwar cibiyar, za ta samar da cikakkiyar kulawa ta musamman ga saran maciji da sauran batutuwan da suka shafi gudanar da bincike a kan cututtukan da suka shafi maciji, rigakafi, tantancewa da magani, tabbatar da samun ci gaba mai ɗorewa da samar da ingantaccen maganin dafin maciji da kuma samun cikakken sashin asibiti da na likitanci, domin inganta kula da majinyata da ayyukan ƙwararru da sauran makamantansu.

“Haka zalika kuma, za ta yi haɗin gwiwa da cibiyoyin ƙasa da ƙasa. Wannan babban mataki ne da ya kawo wata cibiya da za ta kasance irinta ta farko a faɗin ƙasar nan, amma kuma a yankinmu.”

Pate ya kuma ce, abu na biyu shi ne; amincewa da sayen motocin asibiti guda 10 da ke ba da gudummawar jini, domin ayyukan shiyya na hukumar kula da jini ta ƙasa, don sauƙaƙa saye, tara da rarraba jini a kowace shiyya.

Ya ce, Nijeriya na buƙatar gudummawar jini kimanin miliyan 1.8 a duk shekara, inda ya ƙara da cewa; a halin yanzu, ƙasar na samun kusan kashi 25 zuwa 30 ne kacal.

“Za a iya tura waɗannan motoci na ba da gudummawar jini, don tara masu ba da gudummawa, ta yadda za mu inganta tarin jini mai muhimmanci ga mata masu juna biyu, ga waɗanda suka ji rauni da waɗanda aka yi wa tiyata ko kuma ga waɗanda ake yi wa tiyata, amma kuma ga waɗanda ake jinyar cutar daji, waɗanda ke buƙatar ƙarin jini ko wasu abubuwa na jini.

Amince
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

MASU ALAKA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036
Labarai

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Next Post
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

LABARAI MASU NASABA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.