Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ƙaddamar da tallafin Ramadan ga marasa galihu, ’yan gudun hijira da masu lalura ta musamman 43,000 domin sauƙaƙa musu gudanar da azumi. Tallafin ya shafi ’yan gudun hijira 35,000 da kuma masu lalura ta musamman 8,000 a dukkan ƙananan hukumomi 23 na jihar.
Da yake ƙaddamar da shirin a ranar Asabar, Gwamna Ahmad Aliyu ya ce tallafin na daga cikin manufofin gwamnatinsa na tallafa wa mabukata a watan Ramadan. Mataimakinsa, Idris Muhammad Gobir, ne ya wakilce shi a wajen taron.
- Zaɓen Mazaɓu Na APC A Sakkwato Alama Ce Ta Haɗin Kai
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto ’Yan Kasuwa A Sakkwato
A cewarsa, kowane wanda ya amfana zai samu buhun shinkafa guda, kayan Sallah da kuma Naira 5,000 domin rage musu radadin halin da suke ciki a lokacin azumi da bukukuwan Sallah.
Gwamnatin ta kuma jaddada aniyarta na ci gaba da kula da ’yan gudun hijira, tare da haɗa kai da hukumomin tsaro domin tabbatar da kariyarsu da kuma ƙoƙarin mayar da su garuruwansu na asali idan yanayi ya daidaita.















Discussion about this post