Tsohon shugaban hukumar kula da alhazai ta kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Sale Usman Pakistan ya bayyana cewa a baya harkar daba da ke faruwa a yanzu a wasu unguwannin Jihar Kano, ba a san Kano da ita ba, saboda Kano gari ne na zaman lafiya.
Farfesa Pakistan ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a gidansa da ke unguwar Tudun Murtala a Kano.
Haka kuma Farfesa Pakistan ya ce zai yi wuya ka samu dan da yake girmama iyaye irin mutanan Kano, amma a ce an samu wadanda za su bijirewa kowa, to wanan bai dace ba.
Shehin malamin ya ce irin wannan abu da matasan ke yi bai kamata ba a zura masu ido ba, dole sai an zauna da su an ji matsalolinsu ba wai a rika hadasu da hukumomin tsaro ba.
Irin wannan ya sa kungiyar ci gaban unguwar Tudun Murtala ta yi zama da irin wadanann matasa domin jin matsalolin da ke addabarsu. Matasan sun shaida masu cewa rashin aikin yi na daya daga cikin abin ya jefa su shiga wannan hali na fadace-fadacen daba.
Farfesa Pakistan ya ce sakamakon haka ya sa suka kafa gidauniyar da za ta taimaka masu wajen samar masu da aiki da kuma ilimi da sauransu, yanzu haka kuma shiri ya yi nisa.
Sai ya yi kira ga sauran unguwannin Kano da su kafa gidauniya irin wannan da nufin taimaka wa matasa, saboda bai kamata a rika tsanan irin wadannan matasa ba, yana da kyau da kuma muhimmanci a rika jawo su a jiki maimakon tsanar su.













