ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

by Alhassan Suleiman Dakace
43 minutes ago
Kano

Tsohon shugaban hukumar kula da alhazai ta kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Sale Usman Pakistan ya bayyana cewa a baya harkar daba da ke faruwa a yanzu a wasu unguwannin Jihar Kano, ba a san Kano da ita ba, saboda Kano gari ne na zaman lafiya.

Farfesa Pakistan ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a gidansa da ke unguwar Tudun Murtala a Kano.

Haka kuma Farfesa Pakistan ya ce zai yi wuya ka samu dan da yake girmama iyaye irin mutanan Kano, amma a ce an samu wadanda za su bijirewa kowa, to wanan bai dace ba.

ADVERTISEMENT

Shehin malamin ya ce irin wannan abu da matasan ke yi bai kamata ba a zura masu ido ba, dole sai an zauna da su an ji matsalolinsu ba wai a rika hadasu da hukumomin tsaro ba.

 Irin wannan ya sa kungiyar ci gaban unguwar Tudun Murtala ta yi zama da irin wadanann matasa domin jin matsalolin da ke addabarsu. Matasan sun shaida masu cewa rashin aikin yi na daya daga cikin abin ya jefa su shiga wannan hali na fadace-fadacen daba.

LABARAI MASU NASABA

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Farfesa Pakistan ya ce sakamakon haka ya sa suka kafa gidauniyar da za ta taimaka masu wajen samar masu da aiki da kuma ilimi da sauransu, yanzu haka kuma shiri ya yi nisa.

Sai ya yi kira ga sauran unguwannin Kano da su kafa gidauniya irin wannan da nufin taimaka wa matasa, saboda bai kamata a rika tsanan irin wadannan matasa ba, yana da kyau da kuma muhimmanci a rika jawo su a jiki maimakon tsanar su.

Kano
Alhassan Suleiman Dakace
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
Labarai

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026

LABARAI MASU NASABA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.