ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

by Abubakar Sulaiman
16 seconds ago

Wata ɗaliba mai shekaru 19, Rebecca Kambai, wadda ke karatun mataki na biyar a Jami’ar Tarayya ta Kimiyyar Kiwon Lafiya da ke Azare (FUHSA), ta rasa ranta sakamakon wani hatsarin mota da direban ya tsere daga wurin a kan hanyar Bauchi–Jos a Jihar Bauchi.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata yayin da Rebecca ke dawowa gida bayan karɓo kayanta da aka kawo mata daga makaranta.

Majiyoyin iyalinta sun bayyana cewa Rebecca ta dawo gida hutun makaranta ne, amma daga baya ta gano ta manta wasu kayanta a harabar jami’ar. Abokanta suka shirya aka kawo mata kayan zuwa tashar mota da ke kusa da Awala Hotel a Bauchi, inda ɗan’uwanta ya kai ta a babur domin karɓarsu.

ADVERTISEMENT

Bayan sun karɓi kayan suna kan hanyarsu ta komawa gida ne Rebecca ta karɓi tuƙin babur ɗin, amma da suka isa gaban Police Officers’ Mess a yankin New GRA, wata motar Sharon ta buge su sannan ta tsere.

An ce Rebecca ta buga kanta da ƙasa, lamarin da ya haifar mata da mummunan rauni a ƙoƙon kai wanda ya yi sanadin rasuwarta nan take, yayin da ɗan’uwanta ya samu raunuka.

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Rahoton Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) ya tabbatar da cewa hatsarin ya faru da misalin ƙarfe 5:15 na yamma ranar 14 ga Yuli, 2026, kuma jami’an ceto sun isa wurin cikin mintuna goma bayan samun rahoton.

An garzaya da wanda ya jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) domin kula da lafiyarsa, yayin da aka ajiye gawar Rebecca a ɗakin ajiyar gawa na asibitin.

Mahaifiyar marigayiyar, Doris Kambai, ta bayyana rasuwar ‘yarta a matsayin babban rashi ga iyalinta. Ta ce Rebecca ita ce ƙaramar ‘yarta kuma tana da matuƙar basira da hazaƙa. Ta gode wa duk waɗanda suka jajanta wa iyalinsu tare da yi musu addu’a a wannan lokaci na alhini.

A halin yanzu, direban motar Sharon da ake zargi da haddasa hatsarin ya tsere, yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da ƙoƙarin gano shi tare da cafke shi domin fuskantar hukunci.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

MASU ALAKA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026

LABARAI MASU NASABA

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.