Wata ɗaliba mai shekaru 19, Rebecca Kambai, wadda ke karatun mataki na biyar a Jami’ar Tarayya ta Kimiyyar Kiwon Lafiya da ke Azare (FUHSA), ta rasa ranta sakamakon wani hatsarin mota da direban ya tsere daga wurin a kan hanyar Bauchi–Jos a Jihar Bauchi.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata yayin da Rebecca ke dawowa gida bayan karɓo kayanta da aka kawo mata daga makaranta.
Majiyoyin iyalinta sun bayyana cewa Rebecca ta dawo gida hutun makaranta ne, amma daga baya ta gano ta manta wasu kayanta a harabar jami’ar. Abokanta suka shirya aka kawo mata kayan zuwa tashar mota da ke kusa da Awala Hotel a Bauchi, inda ɗan’uwanta ya kai ta a babur domin karɓarsu.
Bayan sun karɓi kayan suna kan hanyarsu ta komawa gida ne Rebecca ta karɓi tuƙin babur ɗin, amma da suka isa gaban Police Officers’ Mess a yankin New GRA, wata motar Sharon ta buge su sannan ta tsere.
An ce Rebecca ta buga kanta da ƙasa, lamarin da ya haifar mata da mummunan rauni a ƙoƙon kai wanda ya yi sanadin rasuwarta nan take, yayin da ɗan’uwanta ya samu raunuka.
Rahoton Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) ya tabbatar da cewa hatsarin ya faru da misalin ƙarfe 5:15 na yamma ranar 14 ga Yuli, 2026, kuma jami’an ceto sun isa wurin cikin mintuna goma bayan samun rahoton.
An garzaya da wanda ya jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) domin kula da lafiyarsa, yayin da aka ajiye gawar Rebecca a ɗakin ajiyar gawa na asibitin.
Mahaifiyar marigayiyar, Doris Kambai, ta bayyana rasuwar ‘yarta a matsayin babban rashi ga iyalinta. Ta ce Rebecca ita ce ƙaramar ‘yarta kuma tana da matuƙar basira da hazaƙa. Ta gode wa duk waɗanda suka jajanta wa iyalinsu tare da yi musu addu’a a wannan lokaci na alhini.
A halin yanzu, direban motar Sharon da ake zargi da haddasa hatsarin ya tsere, yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da ƙoƙarin gano shi tare da cafke shi domin fuskantar hukunci.













