Yusuf Buhari, ɗan marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya bayyana a hukumance aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai a zaɓen shekarar 2027.
Yusuf, wanda ke riƙe da sarautar gargajiya ta Talban Daura, ya bayyana wannan burin nasa ne a cikin wata wasiƙa da ya sanya hannu da kansa, mai ɗauke da kwanan watan 3 ga Afrilu, 2026, wadda jaridar LEADERSHIP ta gani.
Wasiƙar mai taken “Bayyanar Sha’awar Tsayawa Takarar Kujerar Majalisar Wakilai ta Mazabar Tarayya ta Sandamu/Daura/Mai’adua”, ta bayyana shirin sa na tsayawa takara a ƙarƙashin jam’iyyar APC.
Ya ce: “Cikin girmamawa, ina matuƙar farin ciki na rubuta sha’awata domin sanar da ku aniyata ta tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai a wannan mazaba da aka ambata (Sandamu/Daura/Mai’adua), a ƙarƙashin jam’iyyar APC.”















Discussion about this post