ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, September 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

by Sulaiman
3 days ago
Inec

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) za ta ƙaddamar da wani sabon tsari na musamman, na don bibiyar shirin zaɓen Nijeriya, wanda zai ba hukumar damar sa ido kan shirye-shiryen zaɓe a duk jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya Abuja nan take, yayin da rajistar masu kaɗa ƙuri’a ta kai miliyan 100 gabanin zaɓen 2027.

Shugaban INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan shi ya bayyana haka a ranar Litinin, yayin da yake buɗe taron bita na tsare-tsaren aiki na tsawon kwanaki biyu ga sakataran gudanarwa, wanda aka yi a otal ɗin Marriott da ke Ikeja a Jihar Legas.

Farfesa Amupitan ya ce bitar aikin za ta samar da samfurin bin diddigin aikin mataimakin sakataren gudanarwa na ‘Excel’ da aka daidaita, wanda ke haɗe kai tsaye da allon aikin cibiyar kula da zaɓe na hukumar da kuma tsarin aikin zaɓe.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara cewa hukumar a tarihi ba ta da wata hanya ta musamman da take bin diddigin ayyukan gudanarwa na sakataran gudanarwa, yana bayyana sabon kayan aikin a matsayin wanda zai cike wannan giɓin na hukuma.A cewarsa, idan an tura shi, mai bibiyar zai ba shugabannin zaɓe na jihohi da kwamishinonin masu sa ido da sakataren kwamitin da hedkwata damar ganin rabon kayan aiki, horon wucin-gadi ga ma’aikata da shirin jihohi nan take, yana maye gurbin tsoro saboda rashin sani da sarrafa abubuwa kafin lokaci.

Shugaban INEC ya ce wannan sabuwar hanyar za a yi amfani da ita a zaɓen 2027, tana zama wani tsari na dindindin na koyar da sabbin ma’aikatan gudanarwa a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Fara Sayar Da Hannun Jari Na Naira Tiriliyan 2.15

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

Ya haɗa wannan shiri da ƙoƙarin hukumar na tabbatar da tsabtace rajistar masu kaɗa ƙuri’a da kuma tattara katin zaɓe yayin da rajista ke kusantar miliyan 100, yana bayyana rajistar masu kaɗa ƙuri’a a matsayin ɗaya daga cikin ginshiƙan aiki biyar da ake duba a taron bitar tare da kula da kayan aiki da sarrafa su, fasahar zaɓe, inganta ma’aikata na wucin-gadi, da bin ƙa’idojin kuɗi.

Amupitan ya ce shirin bibiyar zaɓe yana ginuwa ne kan darussan da aka koya daga zaɓukan baya a ƴan kwanakin nan, ciki har da zaɓen gwamnan Jihar Osun, inda kyakkyawan tsari na kayan aiki da fasaha suka samar da sakamako mai kyau.Ya ce hukumar tana aiki yanzu don sanya wannan ƙa’idar ta zama ta ƙasa baki ɗaya a cikin watanni shida da suka rage kafin zaɓen 2027.

A cikin jawabinsa, kwamishinan zaɓe na Jihar Legas ya bayyana taron a matsayin wanda ya zo a kan lokacin da ya kamata a yi shirye-shiryen hukumar, sannan ya yaba wa Tarayyar Turai, ta hanyar tallafin Tarayyar Turai ga mulkin dimokiradiyya a Nijeriya (EU-SDGN), wanda ‘Development Alternatives Incorporated’ (DAI) ke aiwatarwa, kan goyon bayan wannan aiki.

Haka kuma sakataren hukumar, Mrs Rose Oriaran-Anthony, ta ce taron zai tabbatar da cewa shalkwatan hukumar da dukkan jihohi suna aiki ne bisa tsarin ayyukan zaɓe guda, tare da bai wa sakataren gudanarwa ilimi na zamani game da sabbin manufofi, fasaha da hanyoyin gudanarwa kafin zaɓen shekarar 2027.

Ta ce ana sa ran kowace wakilcin jiha zai bar taron bita da rajistar haɗarin kayan aiki, tsari na ɗaukar ma’aikatan wucin-gadi, da shirin haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki na watanni uku masu zuwa, tare da sabon samfuri na bibiyar aiki.

Taron bita da aka shirya ƙarƙashin jagorancin ofishin sakataren hukumar tare da tallafi daga DAI-EUSDGN, ya samu halartar kwamishinonin zaɓe dukkan jihohi da daraktan janar na cibiyar zaɓe da daraktoci daga shalkwatan hukumar da sakatarorin gudanarwa daga jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Inec
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Matatar Dangote Ta Fara Sayar Da Hannun Jari Na Naira Tiriliyan 2.15
  • Sulaiman
    Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum
  • Sulaiman
    CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi
  • Sulaiman
    Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 

MASU ALAKA

Dangote
Labarai

Matatar Dangote Ta Fara Sayar Da Hannun Jari Na Naira Tiriliyan 2.15

September 14, 2026
Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum
Labarai

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

September 14, 2026
Dansanda Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 1 Kan Ya Saki Wani Barawon Mutane A Kano
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 

September 14, 2026
Next Post
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Matatar Dangote Ta Fara Sayar Da Hannun Jari Na Naira Tiriliyan 2.15

September 14, 2026
Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

September 14, 2026
CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

September 14, 2026
Dansanda Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 1 Kan Ya Saki Wani Barawon Mutane A Kano

Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 

September 14, 2026
Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Inec

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Inec

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.