Shugabannin kasashen BRICS a taron kolin kungiyar karo na 18, sun amince da sanarwar hadin gwiwa a New Delhi, babban birnin Indiya, jiya Asabar, inda suka nanata shan alwashinsu na tabbatar da jagorancin duniya mai tafiya da kowa da kowa, da kuma karfafa tsarin mabambantan bangarori.
Kazalika, sun yi kira a kan samar da zaman lafiya da tsaro a fagen kasa da kasa da na yanki, da kuma jaddada batun ci gaban tattalin arzikin duniya mai dorewa da ya kunshi kowa da kowa, kana da karfafa hadin gwiwa tsakanin al’adu da al’ummomi.
Har ila yau, shugabannin sun bayyana cikakken goyon bayansu ga kasar Sin game da shugabancinta na kungiyar BRICS da za ta ja ragama a shekarar 2027 da kuma gudanar da taron kolin BRICS karo na 19 a kasar ta Sin. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














