Kimanin malamai da limamai 3,000 daga ƙananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara sun gudanar da addu’a ta musamman domin samun dawwamammen zaman lafiya a jihar da Nijeriya baki ɗaya, tare da yi wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu addu’ar samun nasara a zaɓen 2027.
An gudanar da addu’ar ne a gidan Darakta-Janar na yaƙin neman zaɓen Tinubu, Sanata Abdul’aziz Yari.
Addu’ar ta kuma mayar da hankali kan sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro da ke yaƙi da rashin tsaro, inda aka roƙi Allah Ya kare su, Ya ba su ƙarfi da nasara wajen fatattakar ’yan ta’adda da ke barazana ga zaman lafiyar ƙasar. Malaman sun kuma yi addu’ar a gudanar da zaɓen 2027 cikin lumana ba tare da rikici ba.
Daga cikin manyan malaman da suka jagoranci addu’ar akwai Sheikh Liman Dan Alhaji daga Babban Masallacin Gusau, wanda ya roƙi Allah Ya sa zaɓen 2027 ya gudana lafiya. Ya kuma yi addu’ar Allah Ya ƙara wa jami’an tsaro ƙarfi wajen dakile duk wani yunƙuri na haddasa rikicin siyasa ko na addini a lokacin zaɓen.
Haka kuma, Sheikh Sadiqu Saddeeq ya yi wa Sanata Yari addu’ar samun nasara wajen gudanar da aikin da Shugaba Tinubu ya ba shi na jagorantar yaƙin neman zaɓen dawowarsa karo na biyu. Ya ce al’ummar Zamfara masu kishin jihar su fahimci cewa aikin babban ƙalubale ne da ya shafi Sanata Yari da kuma jihar baki ɗaya, yana mai cewa: “Dukan idanu yanzu suna kan Sanata Yari.”
A nasa jawabin, Sanata Yari ya roƙi malamai da limamai su ci gaba da wayar da kan al’umma a masallatan Juma’a kan ƙoƙarin da gwamnatin tarayya ke yi wajen magance matsalar tsaro. Ya ce gwamnati na da babban shiri na tura ƙarin sojoji da za su yi aiki a Jihar Zamfara domin magance matsalar tsaro cikin gaggawa. Ya kuma tabbatar da cewa za a ƙara samar da kayan aiki ga jami’an tsaro a jihar da Nijeriya baki ɗaya.














