ADC a jihar Kaduna ta fara wani gagarumin shirin sulhu domin warware rikice-rikicen da suka biyo bayan zabukan fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar gabanin babban zaben shekarar 2027.
Jam’iyyar ta bayyana cewa zabukan fidda gwanin, wadanda suka samar da ’yan takara a mukamai daban-daban na zabe, sun haifar da korafe-korafe a wasu yankuna, lamarin da ya sa wasu daga cikin masu neman takara suka gabatar da koke-koke.
A cikin wata sanarwa da shugaban riko na jam’iyyar, Dakta Bege Katuka, da sakataren jam’iyyar, Mustapha Ahmed, suka sanya wa hannu, ADC ta ce irin wannan yanayi ba sabon abu ba ne a cikin takarar cikin gida ta jam’iyya.
Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa kundin tsarin mulkinta ya tanadi hanyoyi a sarari na magance korafe-korafe da warware sabanin da ka iya tasowa bayan zabukan fidda gwani.















Discussion about this post