Albarkacin ranar tattaunawa tsakanin mabambantan wayewar kai ta duniya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi kira da a inganta fahimtar juna ta hanyar tattaunawa.
A jawabin da ya gabatar jiya Litinin ta kafar bidiyo, Wang Yi ya bukaci dukkanin sassa da su ingiza hadin kai, da neman cimma matsaya ta hanyar musayar fahimta, da ci gaba da karfafa tushen al’adu karbabbu, don gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama, a gabar da ake fuskantar tarin kalubale da ba a taba ganin irinsu ba.
Wang, ya ce kasar Sin ta gabatar da muhimman shawarwari hudu, da nufin ingiza bukatar tattaunawa tsakanin mabambantan wayewar kai. Ya ce da farko kamata ya yi dukkanin sassa su rungumi akidar martaba juna, da ingiza zaman jituwa tsakanin mabambantan wayewar kai. Na biyu kuma, dukkanin sassa su rungumi salon mayar da al’umma gaban komai, da kafa ginshiki mai karfi na gudanar da musaya tsakanin mabambantan wayewar kai. Kana na uku su yi aiki tukuru wajen gado, da wanzar da kirkire-kirkire a fannin al’adun gargajiya, ta yadda hakan zai ingiza wayewar kai da ci gaba.
Kazalika, na hudu, dukkanin sassa su rungumi musaya, da koyi da juna, tare da kyautata tsarin gudanar da tattaunawa tsakanin mabambantan wayewar kai. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post