Manoman Jihar Neja ƙarƙashin Ƙungiyar AFAN sun bayyana goyon bayansu ga ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Bida/Gbako/Katcha, Sa’idu Musa Abdullahi, da gwamnan jihar, Umar Bago, domin sake tsayawa takara a babban zaɓen 2027 mai zuwa.
Manoman, sun sayi fom ɗin nuna sha’awa da na tsayawa takara a ƙarƙashin jam’iyyar APC ne ga ɗan majalisar da gwamnan domin ba su damar shiga zaɓen fidda gwani da kuma babban zaɓe.
Yayin gabatar da fom ɗin ga ɗan majalisar a Abuja, manoman sun bayyana cewa sun sayi fom ɗin ne domin nuna godiyarsu bisa irin kulawa da gudunmawar da ɗan majalisar da gwamnan suka bayar ga harkar noma a jihar.
A cewar manoman, ɗan majalisar babban jigo ne ga manoman jihar, inda suka ce ya gudanar da ayyuka da dama da suka sauƙaƙa harkar noma a jihar, inda ya gina hanyoyin ban ruwa na noman rani a Badegi shi da kansa tare da faɗaɗa aikin zuwa Begi.
Haka kuma, sun ce ya samar da dama ga mata a harkar noma, inda ya ɗauki da dama aiki tare da tura su horo a cibiyar ‘International Institute of Tropical Agriculture’ (IITA).















Discussion about this post