Masu neman takarar gwamnan Jihar Yobe su shida a jam’iyyar APC sun gana da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a ranar Asabar kan rikicin da ke ƙara ƙamari dangane da tsarin zaɓen magajin gwamnati gabanin zaɓen gwamna na shekarar 2027.
Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Hon. Muhammad Ibrahim Bomai; Sanatan Yobe ta Kudu, Lawan Kolo Geidam; tsohon Darakta Janar na NEMA, Injiniya Mustapha Maihaja; tsohon Sufeto Janar na ‘Yansanda, Usman Baba Alkali; Kashim Musa Tumba da Bashir Machina.
An gudanar da taron ne a sirrance a gidan Mataimakin Shugaban Ƙasa da ke Abuja, yayin da ake samun ƙarin rashin jituwa kan amincewa da tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar, Baba Malam Wali, a matsayin wanda APC ta fi so ya zama ɗan takarar gwamna a zaɓen 2027.
Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan warware sabanin da ya biyo bayan zargin zaɓen Wali da kuma nemo hanyoyin tabbatar da haɗin kai a cikin jam’iyyar.
A yayin taron, rahotanni sun ce Shettima ya roƙi ƙungiyar masu neman takarar, wadda aka fi sani da G-6, da su sassauta ra’ayinsu kan tsarin, tare da rungumar tattaunawa domin zaman lafiya da kwanciyar hankali a APC.
A cikin sanarwar bayan taron, masu neman takarar sun bayyana tattaunawar a matsayin mai amfani tare da nuna fatan cewa ci gaba da tuntuba zai taimaka wajen warware matsalar cikin lumana.














Discussion about this post