Hanyar komawar Sanata Ali Ndume zuwa Majalisar Dattawa ta bayyana a sarari bayan babban abokin hamayyarsa wajen neman tikiti a jam’iyyar APC, Honorabul Abdullahi Musa Askira, ya sanar da janyewarsa daga takarar.
An bayyana matakin da Hon. Askira ya ɗauka ne cikin wata sanarwa da mataimakinsa, Bilyaminu Umar Ngulde, ya fitar kuma aka rabawa manema labarai a Abuja.
Hon. Askira ya ce ya janye daga takarar ne bayan roƙo da kiraye-kiraye da dama daga masu ruwa da tsaki na APC a yankin Borno ta Kudu.
ADVERTISEMENT















Discussion about this post