Ana ta ayyururi da lale marhabin da manufar kasar Sin ta nuna zumunci da ’yan uwantaka ga Afirka game da soke harajin kwastam ga kayayyakin kasashen nahiyar masu huldar diflomasiyya da ita, wadda ake dab da fara aiwatarwa daga ranar 1 ga watan Mayun da ke tafe.
Tun daga lokacin da aka sanar da wannan mataki, masana tattalin arziki suna ta tsokaci kan yadda za a ci gajiyar hakan, kasancewar kasar Sin tana da katafariyar kasuwa mai dimbin masu sayayya.
Don haka, wannan wata dama ce da za a yi amfani da ita wajen tsame al’umma bil’adam na nahiyar daga kangin talauci.
A cewar wasu rahotannin dai, sama da mutane miliyan 430 a Afirka na rayuwa cikin matsanancin talauci, wato suna rayuwa da kasa da dala $2.15 a rana, inda hakan ke nuna cewa akwai bukatar yin aiki wurjanjan domin rage radadin talaucin da ke addabar mutane.
Amma bisa samun wannan dama ta soke harajin shigar da kayayyakin Afirka kasuwar kasar Sin, a iya cewa nesa ta zo kusa, domin mafi akasarin talakawan da ke fama da talauci za su samu karin hanyoyin samun kudin shiga musamman ta hanyar noma, kasancewar amfanin gonar kasashen Afirka suna samun matukar karbuwa a kasar Sin.
Sai dai kuma, watakila wani ya yi tunanin cewa zai yi wahala noma ya tsamar da mutane daga talauci a yau, saboda a zamanin yanzu kayayyakin kere-kere sun fi kawo kudin shiga masu yawa.
Tabbas babu tantama, sabbin kere-kere sun fi kawo kudi, to amma mu a Afirka zuwa yanzu, ba mu da kere-keren da za mu iya sayarwa ga kasashen waje, muna fatan hakan nan gaba.
Don haka, abun da muke da shi sai mu yi amfani da shi, kuma tabbas, noma yana sahun gaba, kasancewarsa babbar sana’ar mafi akasarin talakawanmu.Bugu da kari, daga shekarar 1981 zuwa 2021, an kiyasta cewa sama da mutane miliyan 800 a kasar Sin sun fita daga matsanancin talauci, kuma noma ya taka muhimmiyar rawa a wannan nasara, kasancewarsa daya daga manyan hanyoyin samun kudin shiga masu dorewa.
Babban abun da ake bukata shi ne, da farko su kansu talakawan su sauya tunani, su daina ganin hakan ba mai yiwuwa ba ne, su kulla a ransu cewa abun zai yiwu kuma su tsara ayyukansu da kakkarfar niyya da burin samun nasara, kamar yadda masu hikima ke cewa “Allah ya ce tashi in taimake ka”.
Manoman karkara su yi kokarin kafa gamayya mai karfi bisa jagorancin masana ta yadda za su kulla mu’amala da ‘yan kasuwa masu fitar da kayayyaki wadanda za su dora su a kan hanyar yin abubuwan da suka dace, kuma a rike gaskiya da adalci ga kowa.
Daga bangaren gwamnatocinmu kuma, jami’an wayar da kai su sauke nauyin da ke wuyansu na ilmantar da manoma yadda za su ci gajiyar wannan dama da aka samu ta kawo kaya kasar Sin.
Kana a zuba jari a hanyoyin karkara, da ayyukan ban ruwa, da samar da irin shuka mai inganci da kuma kara horar da manoma a kan dabarun noma.
Hakika, idan manoma suka kyautata niyyarsu kana suka samu tallafin da ya dace tun daga kan kayayyakin aiki zuwa hanyoyin sufuri, noma zai zama babbar hanyar cin gajiyar wannan manufa ta kasar Sin ta soke harajin shigo da kayayyakin Afirka cikin katafariyar kasuwarta, inda za a samu fita daga kangin talauci da kaso mai yawa har ma da samun wadataccen abinci a cikin gida. Masu iya magana sun ce, “Noma tushen arziki”. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post