ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Soke Harajin Sin Ga Kasashen Afirka Wata Dama Ce Ta Tsame Mutane Daga Talauci

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago

Ana ta ayyururi da lale marhabin da manufar kasar Sin ta nuna zumunci da ’yan uwantaka ga Afirka game da soke harajin kwastam ga kayayyakin kasashen nahiyar masu huldar diflomasiyya da ita, wadda ake dab da fara aiwatarwa daga ranar 1 ga watan Mayun da ke tafe.

Tun daga lokacin da aka sanar da wannan mataki, masana tattalin arziki suna ta tsokaci kan yadda za a ci gajiyar hakan, kasancewar kasar Sin tana da katafariyar kasuwa mai dimbin masu sayayya.

Don haka, wannan wata dama ce da za a yi amfani da ita wajen tsame al’umma bil’adam na nahiyar daga kangin talauci.

ADVERTISEMENT

A cewar wasu rahotannin dai, sama da mutane miliyan 430 a Afirka na rayuwa cikin matsanancin talauci, wato suna rayuwa da kasa da dala $2.15 a rana, inda hakan ke nuna cewa akwai bukatar yin aiki wurjanjan domin rage radadin talaucin da ke addabar mutane.

Amma bisa samun wannan dama ta soke harajin shigar da kayayyakin Afirka kasuwar kasar Sin, a iya cewa nesa ta zo kusa, domin mafi akasarin talakawan da ke fama da talauci za su samu karin hanyoyin samun kudin shiga musamman ta hanyar noma, kasancewar amfanin gonar kasashen Afirka suna samun matukar karbuwa a kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Sai dai kuma, watakila wani ya yi tunanin cewa zai yi wahala noma ya tsamar da mutane daga talauci a yau, saboda a zamanin yanzu kayayyakin kere-kere sun fi kawo kudin shiga masu yawa.

Tabbas babu tantama, sabbin kere-kere sun fi kawo kudi, to amma mu a Afirka zuwa yanzu, ba mu da kere-keren da za mu iya sayarwa ga kasashen waje, muna fatan hakan nan gaba.

Don haka, abun da muke da shi sai mu yi amfani da shi, kuma tabbas, noma yana sahun gaba, kasancewarsa babbar sana’ar mafi akasarin talakawanmu.Bugu da kari, daga shekarar 1981 zuwa 2021, an kiyasta cewa sama da mutane miliyan 800 a kasar Sin sun fita daga matsanancin talauci, kuma noma ya taka muhimmiyar rawa a wannan nasara, kasancewarsa daya daga manyan hanyoyin samun kudin shiga masu dorewa.

Babban abun da ake bukata shi ne, da farko su kansu talakawan su sauya tunani, su daina ganin hakan ba mai yiwuwa ba ne, su kulla a ransu cewa abun zai yiwu kuma su tsara ayyukansu da kakkarfar niyya da burin samun nasara, kamar yadda masu hikima ke cewa “Allah ya ce tashi in taimake ka”.

Manoman karkara su yi kokarin kafa gamayya mai karfi bisa jagorancin masana ta yadda za su kulla mu’amala da ‘yan kasuwa masu fitar da kayayyaki wadanda za su dora su a kan hanyar yin abubuwan da suka dace, kuma a rike gaskiya da adalci ga kowa.

Daga bangaren gwamnatocinmu kuma, jami’an wayar da kai su sauke nauyin da ke wuyansu na ilmantar da manoma yadda za su ci gajiyar wannan dama da aka samu ta kawo kaya kasar Sin.

Kana a zuba jari a hanyoyin karkara, da ayyukan ban ruwa, da samar da irin shuka mai inganci da kuma kara horar da manoma a kan dabarun noma.

Hakika, idan manoma suka kyautata niyyarsu kana suka samu tallafin da ya dace tun daga kan kayayyakin aiki zuwa hanyoyin sufuri, noma zai zama babbar hanyar cin gajiyar wannan manufa ta kasar Sin ta soke harajin shigo da kayayyakin Afirka cikin katafariyar kasuwarta, inda za a samu fita daga kangin talauci da kaso mai yawa har ma da samun wadataccen abinci a cikin gida. Masu iya magana sun ce, “Noma tushen arziki”. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Hukumar Kula Da Gidaje Ta Jihar Edo Ta Rushe Gine-gine Sama Da 500

Hukumar Kula Da Gidaje Ta Jihar Edo Ta Rushe Gine-gine Sama Da 500

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.