ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Soke Harajin Sin Ga Kasashen Afirka Wata Dama Ce Ta Tsame Mutane Daga Talauci

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 month ago

Ana ta ayyururi da lale marhabin da manufar kasar Sin ta nuna zumunci da ’yan uwantaka ga Afirka game da soke harajin kwastam ga kayayyakin kasashen nahiyar masu huldar diflomasiyya da ita, wadda ake dab da fara aiwatarwa daga ranar 1 ga watan Mayun da ke tafe.

Tun daga lokacin da aka sanar da wannan mataki, masana tattalin arziki suna ta tsokaci kan yadda za a ci gajiyar hakan, kasancewar kasar Sin tana da katafariyar kasuwa mai dimbin masu sayayya.

Don haka, wannan wata dama ce da za a yi amfani da ita wajen tsame al’umma bil’adam na nahiyar daga kangin talauci.

ADVERTISEMENT

A cewar wasu rahotannin dai, sama da mutane miliyan 430 a Afirka na rayuwa cikin matsanancin talauci, wato suna rayuwa da kasa da dala $2.15 a rana, inda hakan ke nuna cewa akwai bukatar yin aiki wurjanjan domin rage radadin talaucin da ke addabar mutane.

Amma bisa samun wannan dama ta soke harajin shigar da kayayyakin Afirka kasuwar kasar Sin, a iya cewa nesa ta zo kusa, domin mafi akasarin talakawan da ke fama da talauci za su samu karin hanyoyin samun kudin shiga musamman ta hanyar noma, kasancewar amfanin gonar kasashen Afirka suna samun matukar karbuwa a kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sai dai kuma, watakila wani ya yi tunanin cewa zai yi wahala noma ya tsamar da mutane daga talauci a yau, saboda a zamanin yanzu kayayyakin kere-kere sun fi kawo kudin shiga masu yawa.

Tabbas babu tantama, sabbin kere-kere sun fi kawo kudi, to amma mu a Afirka zuwa yanzu, ba mu da kere-keren da za mu iya sayarwa ga kasashen waje, muna fatan hakan nan gaba.

Don haka, abun da muke da shi sai mu yi amfani da shi, kuma tabbas, noma yana sahun gaba, kasancewarsa babbar sana’ar mafi akasarin talakawanmu.Bugu da kari, daga shekarar 1981 zuwa 2021, an kiyasta cewa sama da mutane miliyan 800 a kasar Sin sun fita daga matsanancin talauci, kuma noma ya taka muhimmiyar rawa a wannan nasara, kasancewarsa daya daga manyan hanyoyin samun kudin shiga masu dorewa.

Babban abun da ake bukata shi ne, da farko su kansu talakawan su sauya tunani, su daina ganin hakan ba mai yiwuwa ba ne, su kulla a ransu cewa abun zai yiwu kuma su tsara ayyukansu da kakkarfar niyya da burin samun nasara, kamar yadda masu hikima ke cewa “Allah ya ce tashi in taimake ka”.

Manoman karkara su yi kokarin kafa gamayya mai karfi bisa jagorancin masana ta yadda za su kulla mu’amala da ‘yan kasuwa masu fitar da kayayyaki wadanda za su dora su a kan hanyar yin abubuwan da suka dace, kuma a rike gaskiya da adalci ga kowa.

Daga bangaren gwamnatocinmu kuma, jami’an wayar da kai su sauke nauyin da ke wuyansu na ilmantar da manoma yadda za su ci gajiyar wannan dama da aka samu ta kawo kaya kasar Sin.

Kana a zuba jari a hanyoyin karkara, da ayyukan ban ruwa, da samar da irin shuka mai inganci da kuma kara horar da manoma a kan dabarun noma.

Hakika, idan manoma suka kyautata niyyarsu kana suka samu tallafin da ya dace tun daga kan kayayyakin aiki zuwa hanyoyin sufuri, noma zai zama babbar hanyar cin gajiyar wannan manufa ta kasar Sin ta soke harajin shigo da kayayyakin Afirka cikin katafariyar kasuwarta, inda za a samu fita daga kangin talauci da kaso mai yawa har ma da samun wadataccen abinci a cikin gida. Masu iya magana sun ce, “Noma tushen arziki”. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Hukumar Kula Da Gidaje Ta Jihar Edo Ta Rushe Gine-gine Sama Da 500

Hukumar Kula Da Gidaje Ta Jihar Edo Ta Rushe Gine-gine Sama Da 500

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.