ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Soke Harajin Sin Ga Kasashen Afirka Wata Dama Ce Ta Tsame Mutane Daga Talauci

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago

Ana ta ayyururi da lale marhabin da manufar kasar Sin ta nuna zumunci da ’yan uwantaka ga Afirka game da soke harajin kwastam ga kayayyakin kasashen nahiyar masu huldar diflomasiyya da ita, wadda ake dab da fara aiwatarwa daga ranar 1 ga watan Mayun da ke tafe.

Tun daga lokacin da aka sanar da wannan mataki, masana tattalin arziki suna ta tsokaci kan yadda za a ci gajiyar hakan, kasancewar kasar Sin tana da katafariyar kasuwa mai dimbin masu sayayya.

Don haka, wannan wata dama ce da za a yi amfani da ita wajen tsame al’umma bil’adam na nahiyar daga kangin talauci.

ADVERTISEMENT

A cewar wasu rahotannin dai, sama da mutane miliyan 430 a Afirka na rayuwa cikin matsanancin talauci, wato suna rayuwa da kasa da dala $2.15 a rana, inda hakan ke nuna cewa akwai bukatar yin aiki wurjanjan domin rage radadin talaucin da ke addabar mutane.

Amma bisa samun wannan dama ta soke harajin shigar da kayayyakin Afirka kasuwar kasar Sin, a iya cewa nesa ta zo kusa, domin mafi akasarin talakawan da ke fama da talauci za su samu karin hanyoyin samun kudin shiga musamman ta hanyar noma, kasancewar amfanin gonar kasashen Afirka suna samun matukar karbuwa a kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sai dai kuma, watakila wani ya yi tunanin cewa zai yi wahala noma ya tsamar da mutane daga talauci a yau, saboda a zamanin yanzu kayayyakin kere-kere sun fi kawo kudin shiga masu yawa.

Tabbas babu tantama, sabbin kere-kere sun fi kawo kudi, to amma mu a Afirka zuwa yanzu, ba mu da kere-keren da za mu iya sayarwa ga kasashen waje, muna fatan hakan nan gaba.

Don haka, abun da muke da shi sai mu yi amfani da shi, kuma tabbas, noma yana sahun gaba, kasancewarsa babbar sana’ar mafi akasarin talakawanmu.Bugu da kari, daga shekarar 1981 zuwa 2021, an kiyasta cewa sama da mutane miliyan 800 a kasar Sin sun fita daga matsanancin talauci, kuma noma ya taka muhimmiyar rawa a wannan nasara, kasancewarsa daya daga manyan hanyoyin samun kudin shiga masu dorewa.

Babban abun da ake bukata shi ne, da farko su kansu talakawan su sauya tunani, su daina ganin hakan ba mai yiwuwa ba ne, su kulla a ransu cewa abun zai yiwu kuma su tsara ayyukansu da kakkarfar niyya da burin samun nasara, kamar yadda masu hikima ke cewa “Allah ya ce tashi in taimake ka”.

Manoman karkara su yi kokarin kafa gamayya mai karfi bisa jagorancin masana ta yadda za su kulla mu’amala da ‘yan kasuwa masu fitar da kayayyaki wadanda za su dora su a kan hanyar yin abubuwan da suka dace, kuma a rike gaskiya da adalci ga kowa.

Daga bangaren gwamnatocinmu kuma, jami’an wayar da kai su sauke nauyin da ke wuyansu na ilmantar da manoma yadda za su ci gajiyar wannan dama da aka samu ta kawo kaya kasar Sin.

Kana a zuba jari a hanyoyin karkara, da ayyukan ban ruwa, da samar da irin shuka mai inganci da kuma kara horar da manoma a kan dabarun noma.

Hakika, idan manoma suka kyautata niyyarsu kana suka samu tallafin da ya dace tun daga kan kayayyakin aiki zuwa hanyoyin sufuri, noma zai zama babbar hanyar cin gajiyar wannan manufa ta kasar Sin ta soke harajin shigo da kayayyakin Afirka cikin katafariyar kasuwarta, inda za a samu fita daga kangin talauci da kaso mai yawa har ma da samun wadataccen abinci a cikin gida. Masu iya magana sun ce, “Noma tushen arziki”. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

MASU ALAKA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
Next Post
Hukumar Kula Da Gidaje Ta Jihar Edo Ta Rushe Gine-gine Sama Da 500

Hukumar Kula Da Gidaje Ta Jihar Edo Ta Rushe Gine-gine Sama Da 500

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.