ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

by Shuaibu Shuaibu
1 hour ago
NDLEA

Baya ga yawan mutanen da ake kamawa da gurfanarwa a gaba kotu da kuma kwace miyagun kwayoyi, yana da wuya a iya auna nasarar da shugaban hukumar yaki da sha da safarar miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA), Mohammed Marwa, ya samu wajen yaki da miyagun kwayoyi a Nijeriya.

Cikakken bincike da bayanai sun tabbatar da cewa miyagun kwayoyi da ke yawo a kasa nan ba su da yawa idan aka kwatanta rukunin mutane da yankin da miyagun kwayoyi suka fi shafa.

Rashin tsaro da ke addabar kasar nan an danganta shi da ayyukan ma’adinai, talauci, ta’addanci, canjin yanayi da kuma takaddama a tsakanin manoma da makiyayi.

ADVERTISEMENT

Dangantaka da kasuwancin miyagun kwayoyi, duk da haka ba a ba ta kulawar da ta dace. Ta’ammuli da miyagun kwayoyi da safarar miyagun kwayoyi na taka muhimmiyar rawa a manufofin kan yadda za a warware matsalolin tsaro na kasar nan.

A duk duniya, haramtacciyar kasuwancin miyagun kwayoyi na tafiyar da hanyar sadarwa da ta shafi nahiyoyi biyar, yana samar da biliyoyin daloli a matsayin kudaden shiga kuma yana hallaka rayukan miliyoyin mutane.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

Mafi yawan masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi na yankin Arewacin Amurka da Turai. Amma a Nijeriya, kamar sauran kasashen Yammacin Afirka, tana kara zama wurin kasuwaci har ma da masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi, wanda hakan ke kara haddasa tashin hankali da rashin tsaro.

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke yaki da miyagun kwayoyi da laifuka ya kiyasta cewa tan 50 na hotar Iblis daga kudancin Amurka yake fitowa, musamman kasar Colombiya, wanda ake safarar shi zuwa Yammacin Afirka a kowace shekara.

Amma a sabon bincike, an kwato kusan tan 31 na hotar Iblis daga wata jirgi a bakin tekun Yammacin Afirka.

Sai dai NDLEA tana ganin babu shaidar cewa manyan masu safarar miyagun kwayoyi na Kudancin Amurka suna aiki yanzu a Nijeriya, amma ta amincewa cewa wasu na iya kokarin samun wasu miyagun kwayoyi hanyar abokan hulda na cikin gida.

Shugaban hukumar NDLEA, ya fusata da wadannan matakan. Hukumar ta bayar da rahoto a cikin ‘yan makonnin da suka gabata game da rushewar tsarin hadin gwiwar mutanen, kafin lamarin ya ta’azzara.

An tarwatsa dakunan sarrafa kwayar methamphetamine guda biyu a cikin dazuzzukan jihohin Ogun da Oyo, in ji mai magana da yawun hukumar NDLEA, Femi Babafemi.

Abin da yake bayyana a matsayin sabon abu shi ne, har da ‘yan kasar Medico a cikin wadada aka kama a dakunan sarrafa miyagun kwayoyi. An kama su tare da manyan dillalan miyagun kwayoyi da ke Nijeriya.

Da yawa ‘yan Nijeriya na son karin bayani game da wadannan baki da ke kafa dakunan sarrafa miyagun kwayoyi a kasar, ko za a gurfanar da su a kotu ko kuma a ba su damar komawa kasashensu lafiya.

NDLEA ta ce tana da cibiyar sadarwa ta duniya na abokan hulda da abokan aiki inda ake raba bayanan sirri akai-akai kan motsin mutanen.

Babafemi yana yawan cewa NDLEA na aiki tare da mafi yawancin manyan hukumomin tsaro na duniya, musamman takwarorinsu na Amurka, Birtaniya, Kanada, Faransa, Jamus, Brazil, Indiya, Saudiyya, Switzerland, Girka, Afirka ta Kudu, Gambiya da Ghana.

Amma yadda wasu daga cikin ‘yan Medican da aka kama kwanan nan suna sarrafa da miyagun kwayoyi tare da safararsu suka shigo Nijeriya har yanzu ba a bayyana ba. NDLEA na cewa suna samun taimako mai yawa daga ofisoshin jakadancin Nijeriya a kasashen waje.

Amma a bayyane yake ana son jami’an NDLEA su kasance wakilan kasar a wasu daga kasashen waje, musamman a kasashen da ake sarrafa miyagun kwayoyi, kamar yadda wasu kasashe suke da jami’an wakilansu a Nijeriya.

NDLEA
Shuaibu Shuaibu
+ postsBio
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

MASU ALAKA

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba
Bakon Marubuci

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
Next Post
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.