Gamayyar Kungiyoyin Tabbatar da Sauye-Sauye ta Kasa wato NCTR, sun jinjina wa Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho, kan sabbin sauye-sauyen da ya kirkiro da su, a Hukumar, a karkashin shugabancinsa.
A cewarsu, wadannan sauye-sauyen da Dantso ya kirkiro da su a NPA, tuni, kwalliya ta fara biyan kudin Sabulu, a fannin na sufurin Jiragen Ruwan kasar.
Sun yi nuni da cewam nadin da Shugaban kasa Bola Tinubu ya yiwa Dantsoho, a matsayin shugaban NPA bai yi zaben Tunun dare ba, musamman duba da irin kyawawan sauye-sauyen da Dantsoho, ya samar da fannin.
Kungiyoyin sun kara da cewa, wadannan sabbin sauye-sauyen, sun kuma kara karfafa gudanar da ayyukan NPA tare da kara karfafawa alummar kasar, guiwa, musamman yadda Dantsoho, ya zamanantar da ayyukan NPA
Babban Daraktan gamayyar kungiyoyin Dakta Richard Ocheje, ya bayyana haka, a cikin sanawar da ya fitar a Abuja, inda kuma ya yabawa gwamnatin shugaba Tinubu, kan wanzar da tsare-tsaren da suka saita fannin sufurin Jiragen Ruwan kasa, musamman yadda ake ci gaba da zuba jari da kara tabbatar da gasa da kuma kara habaka fannin tattalin arzikin Nijeriya.
A cewar Ocheje, sauye-sauyen wadanda suka karade kowanne bangare, musamman na samar da kayan aiki na zamani ga NPA, sun kara taimaka wa, wajen kara ingnata ayyukan NPA, tare da daga darajar NPA, musamman a yankin Afirka ta Tsakiya
Ya kara da cewa, Hukumar a karkashin shugabancin Dantsoho, ta kirkiro da shiye-shiryen da suka kara bunkasa ayyukanta, musamman duba da yadda suka kara bunkasa kokarin da gwamnatin kasar ke ci gaba da yi, na tabatar da ana yin gaskiya, wajen tafiyar da ayyukan NPA.
“A cikin dan karamin lokaci, NPA a samu nasarar daga kimar ta, musamman a matsayina na Hukumar da ke sanya ido a tafiyar da ayyukan Hukumar,” A Ocheje.
Ya ci gaba da cewa, samar da shirye-shiryen ayyukan zamantar da NPA, sun kara taimaka wa, wajen zuba jari, a fannin.
A cewarsa, yarjejeniyar Fam miliyan 746 na kudin Ingila da aka rattaba hannu a watan Maris din 2026, ana sa ran, za ta taimaka wa, aikin zamanantar da Tashishin Jiragen Ruwa na Apapa da Tin Can Island, da ke a jihar the Legas.
Kazalika, ya ce, gwamnatin tarayya na shirin kashe dala biliyan daya, a cikin shirin aikin Tashoshin Apapa, Tin Can Island, Kalabar, Warri, Fatakwal da kuma na Onne.
Ocheje ya kara da cewa, gwamnatin shirin fara yin aikin wasu Tashohin na Badagry, Olokola, Ibom, Bakassi da Bonny, wadanda za su kara taimaka wa, ayyukan na NPA.
Ya kuma yabawa gwamnatin, kan zamantar da ayyukan NPA, musamman kan tsarin NSW, wanda ya ce, hakan ya taimaka, wajen rage jinkirin kawar da kayan da aka yo jigilarsu da kuma kara bunkasa hada-hadar kasuwanci.
Ya kuma bayyana jin dadinsa kan gabatar da kudurin kafa Hukumar Sanya Ido kan fannin tattalin arzikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar wato NPERA da Majalisar kasar ta yi.
A cewarsa, idan aka amince da kafa wannnan Hukumar, musamman ta kasance mai cin gashin kanta, zai taimaka wajen sanya ido na kudin harajin da ake karba a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar da kuma kara ingnata ayyukan NPA.
Kazalika, gunyiyoyin sun bayyana cewa, wanzar da sauyen-sauyen da ake ci gaba da yi a NPA. Za su kara taimaka wa, wajen samar da saukin yin kasuwanci, janyo hankalin masu zuba jari da suransu.
Tuni dai, gwamnatin kasar, ta ayyana fannin kusanci na take a matsayin wani bangare na kara habaka fannin tattalin arzikin kasar.
Tun bayan kafa ma’aikatar ta bunkasa tattalin arzikin Teku a 2023, gwamnatin kasar ta kirikiro da shirye-shirye da dama, tare da daga darajar kayan aiki da kuma kula da shige da ficen kayan da ake shigowa da zuwa Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.














