ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

by Abubakar Abba
1 day ago
NPA

Gamayyar Kungiyoyin Tabbatar da Sauye-Sauye ta Kasa wato NCTR, sun jinjina wa Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho, kan sabbin sauye-sauyen da ya kirkiro da su, a Hukumar, a karkashin shugabancinsa.

A cewarsu, wadannan sauye-sauyen da Dantso ya kirkiro da su a NPA, tuni, kwalliya ta fara biyan kudin Sabulu, a fannin na sufurin Jiragen Ruwan kasar.

Sun yi nuni da cewam nadin da Shugaban kasa Bola Tinubu ya yiwa Dantsoho, a matsayin shugaban NPA bai yi zaben Tunun dare ba, musamman duba da irin kyawawan sauye-sauyen da Dantsoho, ya samar da fannin.

ADVERTISEMENT

Kungiyoyin sun kara da cewa, wadannan sabbin sauye-sauyen, sun kuma kara karfafa gudanar da ayyukan NPA tare da kara karfafawa alummar kasar, guiwa, musamman yadda Dantsoho, ya zamanantar da ayyukan NPA

Babban Daraktan gamayyar kungiyoyin Dakta Richard Ocheje, ya bayyana haka, a cikin sanawar da ya fitar a Abuja, inda kuma ya yabawa  gwamnatin shugaba Tinubu, kan wanzar da tsare-tsaren da suka saita fannin sufurin Jiragen Ruwan kasa, musamman yadda ake ci gaba da zuba jari da kara tabbatar da gasa da kuma kara habaka fannin tattalin arzikin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

A cewar Ocheje, sauye-sauyen wadanda suka karade kowanne bangare, musamman na samar da kayan aiki na zamani ga NPA, sun kara taimaka wa, wajen kara ingnata ayyukan NPA, tare da daga darajar NPA, musamman a yankin Afirka ta Tsakiya

Ya kara da cewa, Hukumar a karkashin shugabancin Dantsoho, ta kirkiro da shiye-shiryen da suka kara bunkasa ayyukanta, musamman duba da yadda suka kara bunkasa kokarin da gwamnatin kasar ke ci gaba da yi, na tabatar da ana yin gaskiya, wajen tafiyar da ayyukan NPA.

“A cikin dan karamin lokaci, NPA a samu nasarar daga kimar ta, musamman a matsayina na Hukumar da ke sanya ido a tafiyar da ayyukan Hukumar,” A Ocheje.

Ya ci gaba da cewa, samar da shirye-shiryen ayyukan zamantar da NPA, sun kara taimaka wa, wajen zuba jari, a fannin.

A cewarsa, yarjejeniyar Fam miliyan 746 na kudin Ingila  da aka rattaba hannu a watan Maris din 2026, ana sa ran, za ta taimaka wa, aikin zamanantar da Tashishin Jiragen Ruwa na Apapa da Tin Can Island, da ke a jihar the Legas.

Kazalika, ya ce, gwamnatin tarayya na shirin kashe dala biliyan daya, a cikin shirin aikin Tashoshin Apapa, Tin Can Island, Kalabar, Warri, Fatakwal  da kuma na Onne.

Ocheje ya kara da cewa, gwamnatin shirin fara yin aikin wasu Tashohin na Badagry, Olokola, Ibom, Bakassi da Bonny, wadanda za su kara taimaka wa, ayyukan na NPA.

Ya kuma yabawa gwamnatin, kan zamantar da ayyukan NPA, musamman kan tsarin NSW, wanda ya ce, hakan ya taimaka, wajen rage jinkirin kawar da kayan da aka yo jigilarsu da kuma kara bunkasa hada-hadar kasuwanci.

Ya kuma bayyana jin dadinsa kan gabatar da kudurin kafa Hukumar Sanya Ido kan fannin tattalin arzikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar wato NPERA da Majalisar kasar ta yi.

A cewarsa, idan aka amince da kafa wannnan Hukumar, musamman ta kasance mai cin gashin kanta, zai taimaka wajen sanya ido na kudin harajin da ake karba a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar da kuma kara ingnata ayyukan NPA.

Kazalika, gunyiyoyin sun bayyana cewa, wanzar da sauyen-sauyen da ake ci gaba da yi a NPA. Za su kara taimaka wa, wajen samar da saukin yin kasuwanci, janyo hankalin masu zuba jari da suransu.

Tuni dai, gwamnatin kasar, ta ayyana fannin kusanci na take a matsayin wani bangare na kara habaka fannin tattalin arzikin kasar.

Tun bayan kafa ma’aikatar ta bunkasa tattalin arzikin Teku a 2023,  gwamnatin kasar ta kirikiro da shirye-shirye da dama, tare da daga darajar kayan aiki da kuma kula da shige da ficen kayan da ake shigowa da zuwa Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.

NPA
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.