Gwamnatin Jihar Kogi ta sanar da ceto mutane huɗu da aka yi garkuwa da su yayin harin da aka kai wata cibiyar rubuta jarabawar NECO da ba ta da izini a garin Olowa, cikin Ƙaramar Hukumar Dekina. Waɗanda aka ceto sun haɗa da shugaban makarantar, da wani jami’in Hukumar Shirya Jarabawar NECO, da ɗalibai biyu.
Kwamishinan Yaɗa Labarai da Sadarwa na jihar, Kingsley Femi Fanwo, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa Gwamna Ahmed Usman Ododo ya ba da umarnin gaggauta gudanar da aikin ceto nan da nan bayan aukuwar lamarin.
Ya ce Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Tsaro, Kwamanda Jerry Omodara (mai ritaya), ne ya jagoranci haɗin gwiwar rundunar sojoji, da DSS, da ƴansanda da jami’an tsaron sa-kai wajen gudanar da aikin.
A cewar Fanwo, jami’an tsaron sun mamaye dazukan da ake zargin masu garkuwar sun ɓoye waɗanda suka sace, lamarin da ya tilasta wa masu laifin tserewa tare da barin mutanen da suka yi garkuwa da su. Ya tabbatar da cewa an haɗa waɗanda aka ceto da jami’an tsaro domin yi musu tambayoyi da kuma duba lafiyarsu, inda ya ce dukkansu na cikin ƙoshin lafiya.
Gwamnatin jihar ta ce jami’an tsaro na ci gaba da sintiri a cikin dazukan domin kamo waɗanda suka tsere. Ta kuma yabawa Rundunar Sojin Najeriya, DSS, Rundunar ‘Yansanda, jami’an tsaron sa-kai da sauran hukumomin tsaro bisa haɗin kai da suka nuna.
Haka kuma, gwamnatin ta gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa umarnin da ya bayar ga hukumomin tsaro na ƙasa su bai wa Jihar Kogi cikakken goyon baya wajen ceto mutanen, tare da jaddada cewa za ta ci gaba da ƙarfafa tattara bayanan sirri da haɗin gwiwar jami’an tsaro domin yaƙi da ayyukan ta’addanci a faɗin jihar.














