ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

by Shuaibu Shuaibu
21 minutes ago
Kano

Bisa ga abubuwan da ke faruwa a jam’iyyar adawa ta ADC, rushe shugabancin jam’iyyar a jihar da bakon fuska da aka gani a matsayin dan takarar gwamnan jam’iyyar a Kano, zaben shekarar 2027 na bayyana kamar wacce za ta kasance mai cike da tashin rudani, gasa da rashin tabbas kamar yadda zabukan baya suka kasance a jihar.

Shahararriyar ‘yar jam’iyyar ADC, Naja’atu Mohammed, ta fito karara ta bayyana cewa jam’iyyar ba ta da niyyar ba Ibrahim Khalil tikitin takarar gwamna saboda yana da alaka da Shugaban kasa Bola Tinubu.

Wannan ya sa jam’iyyar ta bai wa babban abokin takararsa, Ibrahim Al Amin, wanda aka fi sani da Ibrahim Little. Idan ADC ta ci gaba ta bai wa Little tikitin takarar jam’iyyar, hakan zai zama babban rarrabuwar kai a jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Little bai taba lashe zaben fitar da gwani ba, ma’ana bai taba samun nasara a zabe ba. Ibrahim Shekarau ya yi nasara a kansa a 2003 waje samun tikitin takarar jam’iyyar APP, kuma Rabiu Kwankwaso ya yi nasara a kansa a 2007 na samun tikitin takarar a jam’iyyar PDP, sannan ya sake rasa tikitin a jam’iyyar a 2023.

Dalili daya shi ne, bai taba samun goyon bayan wakilan jam’iyyar da manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyya ba.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

Amma wannan ba shi ne duka labarin siyasar Ibrahim Little ba, yana da kuzari da fasahar jan hankali, musamman ga matasa. A cewar mutane da dama da ya yi mu’amaloli da su, sun ce yana daya daga cikin ‘yan siyasa masu bai wa a Nijeriya da ba su taba samun nasara a zabe ba.

Watakila a karon farko a siyasarsa, Little zai samu damar gwada tashirinsa a wajen jam’iyya da ya dade yana hana shi samun tikitin takarar gwamna.

Jam’iyyun adawa a kasar nan sun sau rarrabuwan kai. Ya dangane da wanda aka tambaya, laifin hakan yana kan Atiku Abubakar ne, wanda ke dage wajen neman shugabanci duk da ya san cewa wa’adin na yanki kudu ne.

Wasu suna zargin Peter Obi da Kwankwaso da karya hadin kan ‘yan adawa da kuma komawa jam’iyyar NDC. Haka kuma wani bangare na laifin an dora wa Shugaba Tinubu don jawo rikici da kuma kawo cikas a bangaren shari’a ga jam’iyyun adawa.

Amma duk da wannan hayaniyar, siyasar Kano ba ta taba rashin samun gazawa ba wajen yin tsananin gasa. Hanyar da Gwamna Abba Yusuf da Rabiu Kwankwaso suka rabu da juna da kuma canjin jam’iyoyinsu daban-daban ya kunna wutar gasar kujerar gwamna a 2027.

Amma sai dai zabin Kwankwaso na sanya sunan dan takarar gwamnan NDC da abokin takararsa ya rage kwarin giwa.

Akwai yiwuwar fitowar Little a matsayin dan takarar ADC ya kara sabon sauyi a siyasar 2027 a jihar. Yanzu gwagwarmaya ta rabu zuwa gida uku, inda gwamna mai mulkin Abba ke fafatawa da bangaren Kwankwaso da kuma kokarin Little na jawo jama’a daga tushe.

Kano
Shuaibu Shuaibu
+ postsBio
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

MASU ALAKA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
Bakon Marubuci

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.