Bisa ga abubuwan da ke faruwa a jam’iyyar adawa ta ADC, rushe shugabancin jam’iyyar a jihar da bakon fuska da aka gani a matsayin dan takarar gwamnan jam’iyyar a Kano, zaben shekarar 2027 na bayyana kamar wacce za ta kasance mai cike da tashin rudani, gasa da rashin tabbas kamar yadda zabukan baya suka kasance a jihar.
Shahararriyar ‘yar jam’iyyar ADC, Naja’atu Mohammed, ta fito karara ta bayyana cewa jam’iyyar ba ta da niyyar ba Ibrahim Khalil tikitin takarar gwamna saboda yana da alaka da Shugaban kasa Bola Tinubu.
Wannan ya sa jam’iyyar ta bai wa babban abokin takararsa, Ibrahim Al Amin, wanda aka fi sani da Ibrahim Little. Idan ADC ta ci gaba ta bai wa Little tikitin takarar jam’iyyar, hakan zai zama babban rarrabuwar kai a jam’iyyar.
Little bai taba lashe zaben fitar da gwani ba, ma’ana bai taba samun nasara a zabe ba. Ibrahim Shekarau ya yi nasara a kansa a 2003 waje samun tikitin takarar jam’iyyar APP, kuma Rabiu Kwankwaso ya yi nasara a kansa a 2007 na samun tikitin takarar a jam’iyyar PDP, sannan ya sake rasa tikitin a jam’iyyar a 2023.
Dalili daya shi ne, bai taba samun goyon bayan wakilan jam’iyyar da manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyya ba.
Amma wannan ba shi ne duka labarin siyasar Ibrahim Little ba, yana da kuzari da fasahar jan hankali, musamman ga matasa. A cewar mutane da dama da ya yi mu’amaloli da su, sun ce yana daya daga cikin ‘yan siyasa masu bai wa a Nijeriya da ba su taba samun nasara a zabe ba.
Watakila a karon farko a siyasarsa, Little zai samu damar gwada tashirinsa a wajen jam’iyya da ya dade yana hana shi samun tikitin takarar gwamna.
Jam’iyyun adawa a kasar nan sun sau rarrabuwan kai. Ya dangane da wanda aka tambaya, laifin hakan yana kan Atiku Abubakar ne, wanda ke dage wajen neman shugabanci duk da ya san cewa wa’adin na yanki kudu ne.
Wasu suna zargin Peter Obi da Kwankwaso da karya hadin kan ‘yan adawa da kuma komawa jam’iyyar NDC. Haka kuma wani bangare na laifin an dora wa Shugaba Tinubu don jawo rikici da kuma kawo cikas a bangaren shari’a ga jam’iyyun adawa.
Amma duk da wannan hayaniyar, siyasar Kano ba ta taba rashin samun gazawa ba wajen yin tsananin gasa. Hanyar da Gwamna Abba Yusuf da Rabiu Kwankwaso suka rabu da juna da kuma canjin jam’iyoyinsu daban-daban ya kunna wutar gasar kujerar gwamna a 2027.
Amma sai dai zabin Kwankwaso na sanya sunan dan takarar gwamnan NDC da abokin takararsa ya rage kwarin giwa.
Akwai yiwuwar fitowar Little a matsayin dan takarar ADC ya kara sabon sauyi a siyasar 2027 a jihar. Yanzu gwagwarmaya ta rabu zuwa gida uku, inda gwamna mai mulkin Abba ke fafatawa da bangaren Kwankwaso da kuma kokarin Little na jawo jama’a daga tushe.













