Ƙungiyar cigaban mata Manoma (WOFAN) ta ƙaddamar da gada don sauƙaƙa wa masu buƙata ta musamman, da rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana da kuma titin shiga a unguwar Danbare da ke Jihar Kano.
Ayyukan za su amfani dubban mazauna yankin, da ɗaliban makarantar WOFAN Comprehensive School, makarantun da ke kusa da ita da kuma ɗaliban Jami’ar Bayero Kano (BUK).
Wacce ta kafa WOFAN kuma Shugabar Hukumar Gudanarwarta, Dr. Salamatu Garba, ta ce an aiwatar da ayyukan ne bayan tattaunawa da al’umma domin gano matsalolin da suka fi damunsu. Ta bayyana cewa gadar ƙetaren ita ce irinta ta farko a Kano da aka tsara domin masu amfani da keken guragu da sauran masu buƙata ta musamman, yayin da rijiyar burtsatsen ke da wuraren ɗiban ruwa sama da 12.
Da yake ƙaddamar da ayyukan a madadin Gwamnan Kano, Nasiru Isa Dikko, ya yaba wa WOFAN da abokan hulɗarta bisa gudummawar da suka bayar wajen bunƙasa ababen more rayuwa.
Shi ma Mataimakin Shugaban Jami’ar Bayero Kano, Farfesa Haruna Musa, ya ce gadar za ta ƙara tabbatar da lafiyar ɗalibai da sauran masu amfani da hanyar, yayin da shugabannin al’umma suka yi alƙawarin kula da kayayyakin domin su ci gaba da amfani ga jama’a.













