A tsawon shekaru, duk lokacin da aka ambaci Jihar Zamfara a kafafen yada labarai, abin da ya fi zuwa zuciyar mutane shi ne labaran hare-haren ‘yan bindiga, satar mutane domin neman kudin fansa, kashe-kashe da kuma matsalolin tsaro da suka dabaibaye wasu sassan jihar. Wannan yanayi ya sa mutane da dama suka fara kallon Zamfara a matsayin jihar da ta fi fuskantar kalubalen tsaro fiye da yadda ake kallonta a matsayin wata jiha mai albarkatun kasa masu tarin yawa.
Sai dai tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal kan karagar mulki a watan Mayun 2023, an fara ganin sauyi a irin labaran da ake ji daga jihar. Duk da cewa har yanzu akwai kalubalen tsaro da gwamnati ke ci gaba da fuskanta tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro, an fara jin labaran ci gaba, zuba hannun jari, bunkasa tattalin arziki da kokarin amfani da albarkatun kasa wajen inganta rayuwar al’umma.
Daya daga cikin muhimman matakan da gwamnatin Dauda Lawal ta dauka shi ne mayar da hankali kan bunkasa bangaren ma’adanai, wani fanni da masana da masu ruwa da tsaki suka dade suna ganin cewa idan aka tsara shi yadda ya kamata, zai iya zama ginshikin tattalin arzikin jihar da ma kasa baki daya.
Allah Ya albarkaci Jihar Zamfara da dimbin albarkatun ma’adanai. Kusan babu karamar hukuma a jihar da ba ta da nau’in ma’adinan da ake iya hakowa. Daga cikin ma’adanan da jihar ta shahara da su akwai zinariya, ‘lithium’, tantalite da sauran ma’adanai masu matukar amfani ga masana’antu da fasahohin zamani.
Wannan yalwar albarkatun kasa ce ta sa al’ummomi da dama a kauyukan jihar suka dade suna dogaro da hakar ma’adanai domin neman abin masarufi. Amma galibin wannan aiki ana gudanar da shi ne ta hanyar gargajiya, ba tare da isassun kayan aiki na zamani ba, lamarin da ya haifar da asarar rayuka, hadurran rushewar rami da kuma matsalolin muhalli. Duk da irin wadannan hadurran, mutane da dama ba su daina shiga dazuka da wuraren hakar ma’adanai ba saboda neman abin dogaro na rayuwa.
Wata babbar matsala kuma ita ce yawaitar hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba. Tsawon lokaci ana fitar da ma’adanai daga wasu yankunan Zamfara ba tare da tsari ba, abin da ya hana gwamnati samun cikakkiyar riba daga wannan arziki, tare da barin al’ummomin da ke zaune a wuraren hakar ma’adanan ba su amfana yadda ya kamata.
Daga cikin manufofin gwamnatin Dauda Lawal akwai sauya wannan yanayi ta hanyar shigar da harkar ma’adanai cikin ingantaccen tsari. Gwamnatin ta karfafa masu hakar ma’adanai su hadu cikin kungiyoyi tare da yin rajista a matakin jiha da na gwamnatin tarayya domin gudanar da aikinsu bisa doka. Wannan mataki ba wai kawai zai taimaka wajen tabbatar da bin ka’idoji ba ne, har ma zai ba masu hakar ma’adanan damar samun horo, tallafi da kuma kariya a karkashin doka.
Bayan haka, gwamnatin jihar ta fara neman hadin gwiwa da kamfanoni masu zuba jari daga cikin Najeriya da kasashen waje domin jawo manyan masana’antu da za su kara wa ma’adanan jihar kima. Wannan ya nuna sauyi daga tsohon tsarin fitar da danyen ma’adanai zuwa sabon tsari na sarrafa su a cikin gida kafin a kai su kasuwannin duniya.
Wannan yunkuri ya bayyana kwarai a ranar 12 ga Yulin 2026 lokacin da Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci kaddamar da Matatar Hakowa da Sarrafa Ma’adinin Lithium da ke kauyen Boko a Karamar Hukumar Zurmi kamar yadda kakakin gwamnan Sulaiman Bala Idris ya fitar a ranar Lahadi 12 ga Yulin 2026. An gina wannan katafariyar matata ta hannun hadin gwiwar kamfanonin ZAM Mining Company Ltd, Bima Mines Ltd, Jinlide Mining Co. Ltd da sauran abokan hulda kan kudin da ya kai dala miliyan 200.
Wannan ba karamin ci gaba ba ne ga Zamfara. A maimakon a ci gaba da fitar da danyen lithium kawai, kafa matatar na nufin za a fara sarrafa wani bangare na ma’adinan a cikin jihar. Wannan kuwa yana nufin karin darajar tattalin arziki, karin masana’antu, karin haraji ga gwamnati da kuma karin damar ayyukan yi ga matasa.
A jawabinsa yayin kaddamar da matatar, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa ci gaban al’umma ba zai tabbata ba sai idan ana tafiyar da albarkatun kasa cikin gaskiya, adalci da inganci. Ya kuma jaddada cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari tare da tabbatar da cewa ana gudanar da harkokin ma’adanai bisa doka.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa burinsa shi ne sauya harkokin ma’adanai daga tsarin da ba shi da tsari zuwa tsarin da ke samar da karin darajar tattalin arziki. Wannan manufa ta yi daidai da yadda kasashe masu tasowa ke kokarin cin gajiyar albarkatun kasarsu ta hanyar sarrafa su a gida maimakon fitar da su danye.
A yau, lithium ya zama daya daga cikin ma’adanan da duniya ta fi bukata. Ana amfani da shi wajen kera batir na motocin lantarki, na’urorin zamani da kuma tsarin makamashi mai sabuntawa. Saboda haka, samun irin wannan matata a Zamfara na nufin jihar na kokarin shiga cikin wata babbar kasuwa ta duniya da ake hasashen za ta ci gaba da bunkasa cikin shekaru masu zuwa.
Wani muhimmin al’amari da ya kamata a yaba shi ne yadda gwamnatin jihar ta jaddada cewa ba za ta amince da hakar ma’adanai da ta saba wa doka ko kuma ke lalata muhalli ba. Wannan yana nuna cewa manufar gwamnati ba wai kawai samun kudaden shiga ba ce, har ma da tabbatar da dorewar muhalli da kare hakkin al’ummomin da ke rayuwa a yankunan da ake gudanar da ayyukan hakar ma’adanai.
Har ila yau, gwamnatin ta umurci kamfanonin da ke gudanar da ayyukan hakar ma’adanai da su bai wa mutanen yankunan fifiko wajen samar da ayyukan yi, horas da matasa sana’o’i, gudanar da ayyukan raya al’umma da kuma sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na taimaka wa al’ummomin da suke aiki a cikinsu. Idan aka aiwatar da wannan yadda ya kamata, zai taimaka wajen rage zaman banza, kara kudaden shiga na iyalai da kuma rage talauci.
Masu ruwa da tsaki a harkar ma’adanai ma sun bayyana fata kan wannan sabon salo. A wata tattaunawa da LEADERSHIP HAUSA ta yi da Sakataren Kudi na Kungiyar Masu Siyar da Zinariya ta Jihar Zamfara, Aliyu Adamu Almajir, ya bayyana cewa Allah Ya albarkaci kusan dukkan kananan hukumomin jihar da ma’adanai iri-iri. A cewarsa, jawo kamfanonin zuba jari zuwa jihar zai taimaka wajen bunkasa kasuwanci, karfafa tattalin arzikin Zamfara da kuma samar da karin damarmaki ga jama’a. Haka kuma ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta duba yiwuwar tallafa wa masu sana’ar ma’adanai da jari domin su fadada harkokinsu.
Babu shakka, bunkasa fannin ma’adanai ba zai magance dukkan matsalolin Zamfara cikin dare daya ba. Har yanzu akwai bukatar karin tsaro, inganta hanyoyi, samar da wutar lantarki, kare muhalli da kuma tabbatar da cewa ribar da ake samu daga ma’adanai ta isa ga talakawan da ke yankunan da ake hakar su. Haka kuma, akwai bukatar ci gaba da yaki da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba da kuma hana safarar ma’adanai ta haramtacciyar hanya.
Sai dai duk da wadannan kalubale, matakan da gwamnatin Dauda Lawal ta fara dauka sun nuna cewa akwai wani sabon tunani na mayar da albarkatun kasa hanyar bunkasa tattalin arziki maimakon barinsu su ci gaba da zama abin anfani ga wasu kadan.
A karshe, ana iya cewa yunkurin gwamnatin Dauda Lawal na bunkasa bangaren ma’adanai ya fara daukar sabon salo wanda ya hada zuba hannun jari, bin doka, kara wa ma’adanai kima, samar da ayyukan yi da kuma tabbatar da cewa al’ummomin da ke zaune a yankunan ma’adanai sun amfana kai tsaye. Idan aka ci gaba da aiwatar da wadannan manufofi tare da tabbatar da tsaro da gaskiya kamar yadda gwamnan ya jaddada wajen gudanar da harkokin ma’adanai, akwai kyakkyawan fata cewa Zamfara za ta kasance ba wai jihar da ake ambata saboda matsalolin tsaro kawai ba, har ma ta zama abin koyi wajen yadda ake amfani da albarkatun kasa domin gina tattalin arziki mai dorewa da inganta rayuwar al’umma.














