Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ya shigar da ƙarar neman diyyar Naira biliyan 15 a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan Adeyemi Adeniyi, wanda ake bayyanawa a matsayin Darakta Janar na wata hukuma mai suna Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC).
Gbajabiamila ya ce Adeniyi ya ɓata masa suna ne bayan ya zarge shi da neman kashi 48 cikin 100 na wani tallafin fara aiki na Naira biliyan 27.3 da aka ce an ware wa hukumar.
A cikin ƙarar, Gbajabiamila na neman Naira biliyan 10 a matsayin diyya ta gaba ɗaya, Naira biliyan 5 a matsayin ƙarin diyya saboda ɓata suna, da kuma Naira miliyan 200 domin kuɗin shari’a. Haka kuma ya buƙaci kotu ta umarci Adeniyi da ya janye zarge-zargen gaba ɗaya tare da buga ba da haƙuri ba tare da wani sharaɗi ba a manyan jaridun ƙasa guda biyar da kuma dukkan shafukan sada zumunta da aka wallafa zarge-zargen na tsawon kwanaki 30.
Lauyoyin Gbajabiamila sun bayyana zarge-zargen a matsayin ƙarya, marasa tushe kuma masu ɓata suna. A cewarsu, Femi bai taɓa haɗuwa da Adeniyi ba, bai taɓa yin wata mu’amala da shi ba, kuma bai taɓa tura wani mutum ya karɓi kuɗi ko ya nemi cin hanci a madadinsa ba. Ya kuma musanta karɓar Naira miliyan 400 ko neman ƙarin Naira miliyan 200 kamar yadda Adeniyi ya yi ikirari.
Takardun ƙarar sun nuna cewa Adeniyi ya yi waɗannan zarge-zarge ne a wani taron manema labarai, sannan ya maimaita su a wasu kafafen yaɗa labarai. Sai dai Gbajabiamila ya ce ko bayan lauyoyinsa sun aika masa da wasiƙar neman ya janye kalaman nasa tare da ba da haƙuri, ya ci gaba da maimaita zarge-zargen.
Ya ce hakan ya yi matuƙar lalata masa suna da mutuncinsa bayan shekaru da dama yana gudanar da ayyukan gwamnati. Saboda haka, ya buƙaci kotu ta ba shi dukkan buƙatun da ya gabatar, yana mai jaddada cewa zai bar kotu ta tantance gaskiyar lamarin.














